• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wata Sabuwa…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da duniya ke fuskantar manyan sauye-sauye da ba a taba ganin irinsu ba cikin karni, gami da kalubalen annobar COVID-19 da har yanzu ke yaduwa a sassan duniya, a hannu guda masana sun yi gargadi game da yadda yunwa za ta addabi sassan duniya. Wai ana kukan targade sai ga karaya.” 

Kwararru sun sha fadawa shugabannin kasashen duniya a lokuta daban-daban, kafin ma cutar COVID-19 ta zama wani batu na daban cewa, za a fuskanci mummunan matsalar jin kai da ba a taba gani irinta ba, tun a lokacin yakin duniya na biyu saboda wasu dalilai. Kuma yanzu haka, ana fuskantar wannan matsala a yankin kahon Afirka, da ma wasu sassan duniya.

  • Ya Dace A Hukunta Ta’Addancin Da Birtaniya Da Amurka Suka Aikata A Afghanistan

Saboda girman wannan matsala, ofishin kula da harkokin jin kai na MDD (OCHA) ya yi kira da a gaggauta samar da karin kudade, domin tunkarar matsalolin jin kai dake karuwa a yankin kahon Afrika, yayin da yankin ke tsaka da fama da fari. Inda ya yi gargadin cikin rahotonsa na baya-bayan nan da ya fitar a Nairobin Kenya cewa, za a yi asarar rayuka idan ba a samar da karin kudaden ba.

Bayanai na cewa, mutane a yankin kahon Afrika, wadanda ke fama da fari mafi muni da aka gani cikin shekaru 40 da suka gabata, na fuskantar barazanar yunwa, biyo bayan rashin ruwa a damina 4 a jere, a wasu sassan kasashen Habasha da Kenya da Somalia.

Rahoton ya ce, hasashe na nuna cewa, akwai yiwuwar ba za a samu ruwan sama a lokacin damina na bana tsakanin watan Oktoba da Disamba ba, lamarin da zai haifar da iftila’in da ba a taba gani ba. A don haka, akwai bukatar daukar mataki nan take, domin kare matsalolin da ka iya faruwa a watannin dake tafe.

Labarai Masu Nasaba

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Masu lura da al’amuran yau da kullum na cewa, akwai makaurata sama da miliyan 6 da ‘yan gudun hijira fiye da miliyan 3 a yankin kahon Afirka.

Haka kuma akwai wasu miliyoyin al’umma wadanda suke cikin akuba sakamakon bala’un ambaliyar ruwa ko fari. Wannan ita ce aljannar Waina, sama zafi kasa zafi”. Ga matsalar COVID-19, ga kuma wasu matsaloli dake kara kunno kai.

Abun da ya fi muhimmanci yanzu shi ne, ci gaba da tallafawa irin wadannan mutane da suka shiga irin wadannan matsaloli.

Baya ga yadda yaduwar annobar COVID-19 ke haifar da kalubale ga gwamnatocin kasashe daban-daban daga dukkan fannoni, wato daga bangaren lafiyar al’umma, zuwa kawar da talauci da samar da guraban ayyukan yi da isasshen abinci. (Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Da Ke Haifar Da Tashin Hankali A Duniya

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Wanda Ya Dirka Wa Agolarsa Ciki A Ekiti

Related

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
Daga Birnin Sin

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

12 hours ago
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

13 hours ago
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

14 hours ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

16 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

17 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

18 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Wanda Ya Dirka Wa Agolarsa Ciki A Ekiti

'Yansanda Sun Cafke Wanda Ya Dirka Wa Agolarsa Ciki A Ekiti

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.