• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Watakila Rashford Ya Bar Manchester United

by Sulaiman
1 year ago
in Wasanni
0
Watakila Rashford Ya Bar Manchester United
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu dai dan wasa Marcus Rashford, dan kwallon tawagar Ingila, Marcus Rashford wanda ba ya kan ganiya, yana fuskantar kalubale a Manchester United a kakar bana.

Dan wasan mai shekara 26 ya kasa ci gaba da nuna irin kwazon da ya yi a bara, inda ya ci kwallo 30 a dukkan fafatawa a kungiyar kuma Rashford ya taimaka wa United ta dauki Carabao Cup da samun gurbin Champions League a kakar da ta wuce.

  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 
  • AFCON 2023: Masu Masaukin Baƙi Sun Fitar Da Ƙasar Mali

A kakar wasa ta shekara ta 2023 zuwa 2024, ya ci kwallo hudu a wasanni 26 da ya buga wa Manchester United – kenan kwazonsa ya yi kasa sosai, musamman a Premier League.

Saboda haka wasu ke cewa ya kamata Erik ten Hag ya sayar da Rashford ko kungiyar za ta samu kudin sayen wani dan kwallon domin ta kara karfi. To sai dai kuma ba matsalar Rashford kadai United, wadda aka fitar daga Champions League da Carabao Cup da ta dauka a bara ke fustanta ba a kakar nan.

Kungiyar wadda take ta takwas a kan teburin Premier League da maki 32 bayan wasa 21 ta kai zagaye na biyar a FA Cup bayan ta doke kungiyar Newton County a ranar Lahadin da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

A bara ne Rashford ya saka hannu kan yarjejeniyar ci gaba da zama a Manchester United zuwa karshen kakar wasa ta 2028 kan £325,000 a duk mako sannan tun farkon kwantiragin dan kwallon tawagar Ingila zai kare ne a karshen kakar shekara ta 2023 zuwa 2024.

Dan wasan ya taka rawar gani a bara karkashin Erik tten Hag da cin kwallo 30 a wasa 56 a dukkan fafatawa domin ya fara buga wa United wasa a shekarar 2016 a wasa da Midtjylland, kuma kungiyoyi da yawa sun so daukar Rashford a kakar da ta wuce, bayan rawar da ya taka.

Rashford na daya daga cikin ‘yan kwallon Ingila da suka fuskanci kalaman wariya, bayan da ya barar da fenariti a wasan karshe da Italiya a Euro 2020, sannan cikin Agustan shekara ta 2021 ya ji rauni a allon kafada a kakar da ya ci kwallo biyar da ta kai an sallami Ole Gunnar Solskjaer aka maye gurbinsa da Ralf Rangnick.

Bugu da kari, kociyan tawagar Ingila, Gareth Southgate ya ajiye Rashford daga buga wasa hudu a Nations League a cikin watan Yunin shekara ta 2022 sakamakon rashin tabuka abin kirki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: Yadda Abubuwan Mamaki Ke Faruwa A Gasar

Next Post

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujerar Majalisar Tarayya A Jihar Jigawa

Related

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Wasanni

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

12 hours ago
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
Wasanni

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

1 day ago
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON
Wasanni

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

2 days ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

3 days ago
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu
Wasanni

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

5 days ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

5 days ago
Next Post
Gwamnonin PDP Sun Goyi Bayan Kiraye-kirayen Kafa ‘Yansandan Jihohi

Zaɓen Cike-gurbi: PDP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujerar Majalisar Tarayya A Jihar Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.