• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

by Sulaiman
2 months ago
Wike

Ƙungiyar Gwamnonin Jam’iyyar PDP ta yi gargaɗi ga Ministan Abuja, Nyesom Wike, da wasu mambobin jam’iyyar kan yunƙurin da zai iya lalata babban taron jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 ga Nuwamba, 2025.

 

Hakan na cikin sanarwar bayan taron gwamnonin karo na bakwai da aka gudanar a Gusau, Jihar Zamfara, ranar Asabar, 23 ga Agusta, 2025.

  • PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
  • Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

A cewar rahoton gidan talabijin na Channels, gwamnonin sun sake nanata goyon bayan su ga ƙudirin Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na PDP karo na 101 da aka gudanar a watan Yuli, wanda ya amince da shirin babban taron jam’iyyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Taron na Gusau, ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya kuma tattauna kan halin da ƙasar ke ciki, matsalolin tsaro, raguwar darajar Dimokraɗiyya, da shirye-shiryen babban taron PDP mai zuwa.

 

Gwamnonin sun buƙaci mambobin ƙungiyar da su kaurace wa yunƙurin kawo cikas ga taron, inda suka bayyana jam’iyyar PDP a matsayin hanya ɗaya tilo wajen saita Dimokraɗiyya, kuma za ta iya maido da Nijeriya kan turbar shugabanci na-gari da ci gaba.

 

“Zauren ya sake tabbatar da cikakken ƙudurin da aka yi na taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) karo na 101 na Yuli 2025 dangane da babban taron ƙasa na ranar 15 ga Nuwamba.

 

“Muna kira ga mambobin ƙungiyar da su bijire wa duk wani yunƙuri na kawo cikas ga taron da masu adawa da jam’iyya ke yi; amma su ga jam’iyyar PDP a matsayin babbar cibiya ta Dimokraɗiyya da kuma hanyar maido da Nijeriya bisa tafarkin shugabanci nagari da ci gaban ƙasa,” inji wani bangare na sanarwar.

 

Taron wanda shugaban ƙungiyar kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya jagoranta, ya tattauna sosai kan halin da al’umma ke ciki, rashin tsaro, rugujewar tsarin dimokuraɗiyya, da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar na ƙasa da ke tafe.

 

Taron ya yaba da jajircewar shugabanni da mambobin jam’iyyar PDP wajen shawo kan makirce-makircen da aka ƙulla, inda ta jaddada cewa irin waɗannan abubuwan ba za su iya rusa farin jinin da jam’iyyar ba, da ƙoƙarin samar da sauƙin rayuwa da tsaro kamar yadda aka samu a ƙarƙashin gwamnatocin PDP.

 

Gwamnonin sun jaddada aniyarsu ta ceto ƙasar tare da zargin jam’iyyar APC da raba kan gwamnoni da manufofin da ke ci gaba da sanya ‘yan Nijeriya cikin halin ƙunci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro
Manyan Labarai

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
Manyan Labarai

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Next Post
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025
Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi

November 3, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.