• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

  • ‘Yandaba Sun Farwa Tawagar Atiku Farmaki, Mutum 74 Sun Jikkata Suna Asibiti A Borno

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Atiku
Wike da Sauran Gwamnonin G5 yayin da suka ziyarci takwaransu na jihar Bauchi, Gwamna Bala Muhammad Kauran Bauchi

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kasance Ta Farko Wajen Yawaitar Mutane Masu Hazaka A Duniya

Next Post

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

19 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

22 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

1 day ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

3 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

5 days ago
Next Post
Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.