• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Wike: “Yakin Neman Zabe Ne Yanzu A Gaban Mu” – Rundunar Yakin Neman Zaben Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

  • ‘Yandaba Sun Farwa Tawagar Atiku Farmaki, Mutum 74 Sun Jikkata Suna Asibiti A Borno

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Atiku
Wike da Sauran Gwamnonin G5 yayin da suka ziyarci takwaransu na jihar Bauchi, Gwamna Bala Muhammad Kauran Bauchi

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.

An bayyana cewa tuni ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya yi watsi da gaganiyar neman sulhu da Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas da sauran magoya bayan sa.

Wata majiya daga cikin Rundunar Yaƙin Neman Zaɓen Atiku ta shaida wa jaridar Vanguard cewa yanzu Atiku ya maida hankali ne kan yaƙin neman zaɓe, kuma hakan ya yi tasiri sosai, idan aka yi la’akari da irin karɓuwar da ya ke ƙara samu a faɗin ƙasar nan.

“Jirgin yaƙin neman zaɓen Atiku Abubakar na 2023 ya rigaya ya tashi, don haka duk wani tuggu da ƙulle-ƙullen da su Wike za su yi, ba zai haka jirgin kaiwa zango ba.

“Ƙoƙarin da su ka yi da wanda su ke yi domin hana jirgin tashi, bai yi nasara ba. Domin idan ka duba za ka ga a kowane yanki na ƙasar nan Atiku na ci gaba da ƙara samun karɓuwa.

“Wike da sauran gwamnonin da ke goyon bayan sa duk su na da ‘yancin goyon bayan wanda su ka ga dama. Amma fa ba gaskiya ba ce da su ke nuna kan su cewa za su iya hana al’ummar jihohin su zaɓen PDP,” cewar majiyar.

“Maganar cewa su Wike da sauran su na ganin sai wanda su ke so za a zaɓa a jihohin su, wannan duk hauragiya ce kawai. Ka na nufin ka ce Gwamna Seyi Makinde na Oyo na da kwarjinin cewa sai wanda ya ke so za a zaɓa a Oyo? Haba! Shi fa ba Bola Ige ba ne ko Awomolo, to wane kwarjinin hana ‘yan PDP su zaɓi Atiku ya ke da shi?, inji majiyar.

Majiyar ta ce tuni rundunar kamfen ta yi gaba, ba za ta taɓa kowawa kan su Wike ba. “Amma idan mu ka ci karo da su kan hanya, su ka tsayar da jirgin su ka ce a ɗauke su, za mu tsaya su shiga.”

Kwanan nan wasu jiga-jigan PDP da su ka haɗa har da ɗan takarar sanatan Delta ta Tsakiya, Ned Nwoko, sun yi kira ga PDP ta kori Wike, su na cewa ko da shi ko babu shi PDP za ta iya cin zaɓe.

Haka shi ma Gwamna Samuel Ortom na Binuwai, da dama sun ja hankalin sa cewa ya kamata ya yi karatun ta-natsu, ya goyi bayan Atiku Abubakar domin kawo ƙarshen rikice-rikicen makiyaya da manoma a jihar sa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kasance Ta Farko Wajen Yawaitar Mutane Masu Hazaka A Duniya

Next Post

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

5 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

8 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

3 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

3 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

5 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

6 days ago
Next Post
Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

Guterres Ya Yaba Wa Kasar Sin Kan Yadda Take Kokarin Tinkarar Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.