• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wurin Da Ya Fi Ba Ni Wahala A Daukar Shirin Labarina – Hadiza Abubakar

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
11 months ago
in Nishadi
0
Hadiza Abubakar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau ma shafin namu ya yi tozali da wata matashiyar Jarumar mai haskawa cikin masana’antar Kannywood wato, HADIZA ABUBAKAR wacce aka fi sani da UMMI GOMBE. Ta bayyana wa masu karatu yadda aka yi har ta tsinci kanta cikin masana’antar Kannywood, tare da yin kira da ba da shawarwari ga masu kokarin shiga cikin masana’antar tare da sauran abokan sana’arta har ma da wasu batutuwan masu yawa. Ga dai tattaunawar tare da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

Da farko za ki fada wa masu karatu cikakken sunanki tare da sunan da aka fi saninki da shi.

Sunana Hadiza Abubakar wacce aka fi sani da Ummi Gombe.

 

Ko za ki iya fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Kamar yadda na fada a baya sunana Hadiza Abubakar wacce aka fi sani da Ummi Gombe, an haife ni a Kumo Jihar Gombe, kuma na tashi a garin Gombe.

 

A wanne mataki kika tsaya a karatunki?

Na tsaya da karatuna a matakin Sakandare.

 

Ya batun komawa makaranta dan ci gaba da karatu, shin akwai ra’ayin hakan ko babu?

Ina nan ina shiri yanzu haka ma abin da nake kokarin yi kenan.

 

Kin taba yin aure ko tukunna dai?

Eh! Na taba yin aure.

 

Akwai yara ko babu?

Ina da yaro guda daya.

 

Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?

Abin da ya ja hankalina gaskiya ni dai na taso da sha’awar abun ne tun ina karama.

 

Wane rawa ki ke takawa a cikin masana’antar Kannywood?

Ina taka rawar matsayin jaruma.

Hadiza Abubakar

Ya gwagwarmayar shiga cikin masana’antar ta kasance?

An sha gwagwarmaya sosai gaskiya.

 

Lokacin da ki ka fara sanar da iyayenki kina son fara harkar fim, shin kin fuskanci wani kalubale daga gare su ko kuwa?

Ban samu wani kalubale daga gare su sosai ba, addu’a kawai suka yi mun.

 

Za ki yi kamar shekara nawa ko wata nawa da fara fim?

Eh! To, ba zai wuce kamar shekara takwas ba.

 

Da wane fim ki ka fara?

Na fara fitowa a fim din Wuta Biyu.

 

Ya farkon farawar ya kasance?

Kin san duk abin da aka ce farko ne to dole akwai faduwar gaba.

 

Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?

Nayi finafinai masu dan yawa ciki akwai; Bikin Suna, Zabi, da dai sauransu, sannan a yanzu ina daya daga cikin jaruman shiri me dogon zango na Labarina.

 

Wace rawa ki ka taka a cikin shirin Labarina?

Na fito a Yasmeen kawar Maryam.

Hadiza Abubakar

Ta ya kika tsinci kanki a cikin shirin Labarina?

Ina daune Darakta Aminu Saira ya sa aka kira ni aka ce an yi ‘casting’ dina a fim din Labarina.

 

Cikin finafinan da ki ka fito ciki, wanne ne ya zamo bakandamiyarki?

Kowanne amma ina son Labarina.

 

Wane waje ne ya fi burge ki a cikin shirin Labarina?

Wajen da kawata Safina ta sammun Dalar da ta samo.

 

Ko akwai wani waje da ya fi baki wahala cikin finafinan da ki ka fito wanda ba za ki iya mantawa da shi ba?

A cikin shirin Labarina wajen da muka kai Maryam muka fito bayan na sha aiki sai jiri ya biyo baya ga kuma gajiyar aikin da muka gama.

 

Kamar wane irin nasarori kika samu game da fim?

Gaskiya Alhmdulillah na samu nasarori da yawa.

 

Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta cikin masana’antar bayan shigarki?

Ba za a rasa ba tunda a rayuwa ba a rasa kalubale, sai dai na ce Alhamdulillah.

 

Kina da Ubangida a cikin masana’antar Kannywood?

Duk wanda ya taba sani ko niyyar sani ubangidana ne.

 

Wadanne jarumai ne suke burge ki kafin ki fara fim?

Shi fim din ne yake burge ni.

 

Mene ne burinki na gaba game da fim?

Burina shi ne nayi shuhra bayan haka kuma sai aure.

 

Ko akwai wanda ya taba cewa yana son ki cikin masana’antar da har ta kai da kun fara soyayya?

Eh! To, ba za a rasa ba.

 

Kamar wane irin namiji ki ke son aura?

Wanda Allah ya zaba min tunda ba lalle wanda kake so ya zama mafi alkairi a tare da kai ba.

Hadiza Abubakar

Bayan fim kina wata sana’ar ne?

Eh! Ina siyar da kayayyaki kamar su; Atampha, Takalma da sauransu.

 

Ko akwai wani kira da za ki yi ga sauran abokan aikinki?

Ina kira gare su da mu kara hada kanmu mu zama tsintsiya madaurinki daya.

 

Wane irin kira za ki yi ga masu kokarin shiga cikin masana’antar Kannywood?

Kira na ga masu sha’awar shiga masana’antar Kannywood su tabbata da izinin iyayensu za su shiga.

 

Me za ki ce da masoyanki?

Ina yi musu godiya Allah ya bar mu tare kuma idan nayi kuskure su yi kokarin nusar da ni ta yadda zan fahimta.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Ina gaida duk masoyana.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariKannywoodYan matan Film
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Taba Mantawa Da Zamowata Gwarzuwar Banki Sau Biyu A Jere Ba – Fatima Gana

Next Post

Shugaba Bola Tinubu Zai Yi Sauye-Sauye A Gwamnatinsa  Kwanan nan

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

3 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Shugaba Bola Tinubu Zai Yi Sauye-Sauye A Gwamnatinsa  Kwanan nan

Shugaba Bola Tinubu Zai Yi Sauye-Sauye A Gwamnatinsa  Kwanan nan

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.