• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 hours ago
Xi

Da safiyar yau Talata 14 ga watan nan na Oktoba, shugaban kasar Xi Jinping ya gana da takwaransa na Ghana John Dramani Mahama a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, wanda ya zo kasar Sin domin halartar taron kolin mata na duniya.

 

Xi ya bayyana cewa, a bana ake cika shekaru 65 da kafa alakar diflomasiyya tsakanin Sin da Ghana. Ya kuma bukaci bangarorin biyu su tabbatar da sakamakon taron kolin tattaunawa kan hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da binciko hanyoyin hadin gwiwa iri-iri, da fadada hadin gwiwa a fannonin hakar ma’adinai da makamashi da gina kayayyakin more rayuwa, da aikin gona da na kamun kifi.

 

Ya ce bangarorin sun cimma matsaya daya kan tsai da yarjejeniyar raya huldar abota ta ci gaban tattalin arziki a bangaren samun riba a mataki na farko, kana ya yi fatan Ghana za ta samu fa’ida daga matakin Sin na soke haraji kan kayayyakin dake shiga kasar daga kasashen Afirka masu alaka da ita.

LABARAI MASU NASABA

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

 

A nasa bangaren, shugaba Mahama ya taya Sin murnar cimma nasarar gudanar da taron kolin mata na duniya. Yana mai cewa taron yana da muhimmanci, kuma ya bayyana karfin jagorancin Sin na daga matsayin ayyukan mata a duniya. Ya ce Ghana tana da dadaddiyar dangantakar abota da Sin, kana ya godewa Sin saboda goyon baya, da taimako da take baiwa mata karkashin taron FOCAC, da kuma shawarar “ziri daya da hanya daya”. Shugaba na Ghana ya yi fatan kara yin hadin gwiwa da Sin a fannonin kasuwanci, da tattalin arzikin dijital, da gina kayayyakin more rayuwa, da kuma makamashi, da hakar ma’adinai da musayar al’adu, domin inganta dangantakar kasashen biyu.

 

A wannan rana kuwa, shugaba Xi Jinpng ya gana da firaministar kasar Mozambique Maria Benvinda Delfina Levi, wadda take halartar taron koli na mata na duniya dake gudana yanzu haka a birnin Beijing.

 

Yayin zantawarsu, shugaba Xi ya ce a bana ake cika shekaru 50, da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Mozambique, kuma kawancen gargajiya tsakanin sassan biyu ya jure al’amuran kasa da kasa da dama, yana kuma ci gaba da kasancewa mai karfin gaske.

Ya ce Sin a shirye take ta yaukaka goyon bayan juna tare da Mozambique, da karfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare, da fadada hadin gwiwar cimma moriyar juna, da ci gaba da zurfafa cikakkiyar huldar kawance daga dukkanin fannoni, da hada hannu wajen raya sabbin shekaru 50 masu zuwa tare.

A nata bangare kuwa, Levy ta ce jawabin da shugaba Xi Jinping ya gabatar yayin taron koli na mata na duniya dake gudana, na da matukar tasiri da ma’ana. Kuma Mozambique a shirye take ta yi aiki tare da Sin wajen aiwatar da sakamakon taron, da ingiza ci gaban harkokin mata a matakin duniya.(Amina Xu、Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
Daga Birnin Sin

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.