• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Jumma’a 14 ga wata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva, wanda har yanzu ke ziyarar aiki a kasar Sin, a babban dakin taron jama’a.

A yayin shawarwarin, Xi Jinping ya yi maraba da ziyarar Lula a kasar Sin. Ya kuma nuna cewa, kasashen Sin da Brazil su ne manyan kasashe masu tasowa, kuma muhimman kasuwanni masu tasowa a gabashi da yammacin duniya, sun kuma kasance abokan hulda bisa manyan tsare-tsare ga juna, kana suna da moriyar juna a fannoni daban daban.

  • Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar

A cewar shugaba Xi, kasar Sin na sa kaimi ga samun bunkasuwa mai inganci, da bude kofa ga waje bisa babban matsayi, wanda hakan zai kara samar da damammaki ga kasashen duniya ciki har da Brazil. Kaza lika kasar Sin tana son karfafa yin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tare da Brazil, kan batutuwan kasa da kasa dake jawo hankulansu duka, bisa tsarin cudanyar bangarori da dama, ciki har da MDD, BRICS, da G20 da dai sauransu, tare kuma da karfafa hadin gwiwa wajen tinkarar sauyin yanayi.

A nasa bangaren kuwa, shugaba Lula ya bayyana cewa “Wannan ita ce ziyara ta farko a wata kasa da ke wajen nahiyar Amurka, tun bayan da na zama shugaban kasa a wannan karo, wanda ke nuni da irin kaunar da bangaren Brazil ke da shi ga kasar Sin, da kuma muhimmancin da yake ba wa ci gaban dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, kasarsa ta kuduri aniyar bunkasa huldar kut da kut da kasar Sin bisa matsayin manyan tsare-tsare na sa kaimi ga kafa tsarin kasa da kasa mai adalci da ma’ana.

Bayan shawarwarin, shugabannin kasashen biyu sun shaida rattaba hannu kan wasu takardu na hadin gwiwa da suka shafi kasuwanci da zuba jari, da tattalin arziki na zamani, da kirkire-kirkire na kimiyya da fasaha, da watsa labarai da sadarwa, da rage talauci, da binciken annoba da kuma sararin samaniya da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Bugu da kari, bangarorin biyu sun kaddamar da “Sanarwar hadin gwiwa tsakanin Jamhuriyar Jama’ar Sin da Jamhuriyar Tarayyar Brazil, kan zurfafa dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni.” (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babbar Jami’Ar IMF: An Hasashen Cewa Sin Za Ta Ba Da Gudummawar Kusan Kashi 1bisa 3 Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya A Bana

Next Post

Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

Hukunce-Hukuncen Sallar Idi Da Zakatul Fidir

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.