• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
Xi

Da safiyar yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping, tare da takwarorinsa na Rasha Vladimir Putin, da na kasar Mongoliya Ukhnaagiin Khurelsuh, sun gudanar da taro karo na bakwai na shugabannin kasashen Sin, da Rasha, da Mongoliya a babban dakin taron jama’a dake nan birnin Beijing.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, a cikin ’yan shekarun nan, a kai a kai an yi ta samun bunkasar hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin, da Rasha da Mongoliya, kuma an samu sakamako mai inganci. An yi nasarar aiwatar da ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasashen uku, ana kuma ci gaba da samun bunkasar ciniki a tsakanin kasashen uku, kana ana ci gaba da zurfafa hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki, da cinikayya, da kimiyya da fasaha, da kare muhalli, da kuma raya al’adu. A matsayin wata makwabtaciyar abokantaka, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Rasha da Mongoliya wajen tabbatar da ainihin burin hadin gwiwa, da kawar da tsoma baki daga waje, da kuma sa kaimi ga bunkasar hadin gwiwa tsakanin kasashen uku.

A nasa tsokaci, shugaba Putin ya bayyana cewa, kasar Rasha tana son yin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tare da Sin, da Mongoliya a nan gaba, bisa daidaito da cimma moriyar juna, ta yadda za a sanya hadin gwiwar bangarorin uku da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu su dace da juna, kana kuma su habaka juna.

Shi kuwa shugaba Khurelsuh cewa ya yi, bana shekara ce ta cika shekaru 80 da samun nasarar yakin kin hare-haren sojojin Japan da kasar Sin ya gudanar, da babban yakin kishin kasa na Tarayyar Soviet. Don haka ya kamata al’ummomin Mongoliya, Sin, da Rasha su yi murna, da kuma tunawa da wannan lokaci mai cike da tarihi, da kuma yada madaidaicin ra’ayin tarihin yakin duniya na biyu.

Bugu da kari, a safiyar yau, shugaba Xi Jinping ya gana da firaministan Pakistan Muhammad Shahbaz Sharif, da shugaban kasar Uzbekistan Shavkat Miromonovich Mirziyoyev a nan birnin Beijing.(Safiyah Ma)

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Da Afrika Sun Yi Alkawarin Tabbatar Da Nasarar Shirin TVET Na Nahiyar Afrika

October 16, 2025
Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Hukumar FAO Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwa

October 16, 2025
Gaza
Daga Birnin Sin

Wane Ci Gaba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza Ta Haifar?

October 16, 2025
Next Post
Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

Xi: Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.