Da yammacin jiya Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kai rangadin aiki a birnin Rizhao dake lardin Shandong, inda ya ziyarci tashar jiragen ruwa ta Rizhao, da hanyar zirga zirgar mutane ta zirin gabar teku.
Shugaba Xi ya fahimci yadda ake gaggauta raya tashar ba tare da bata muhalli ba kuma bisa fasahohin zamani, da ma yadda birnin ke kara bude kofarta ga ketare, da karfafa kiyaye muhallin gabar tekun, kana da kyautata zaman rayuwar jama’a da sauransu. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp