Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS, kana shugaban hukumar gudanarwar rundunar sojojin kasar Xi Jinping, zai duba faretin sojoji da za a gudanar a nan birnin Beijing a kan titin Chang’an ranar uku ga watan Satumba dake tafe.
Babban jami’i a sashen lura da ayyukan hadin gwiwar rundunonin sojoji, karkashin babban hukumar gudanarwar rundunar sojin kasar ta Sin Wu Zeke ne ya bayyana hakan a Larabar nan, yayin taron manema labarai da ya gudana game da shirye-shiryen gudanar da faretin.
Jami’in ya ce za a gudanar da faretin ne a wani bangare na bikin cika shekaru 80 da cimma nasarar yaki da mamayar dakarun Japan da yakin kin tafarkin murdiya. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp