• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying, ta sanar a yau Jumma’a cewa, bisa gayyatar da takwaransa na kasar Indonesiya Joko Widodo ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai isa tsibirin Bali na kasar Indonesiya, don halartar taron kolin kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki na G20 karo na 17, wanda zai gudana daga ranar 14 zuwa 17 ga watan da muke ciki.

Haka kuma, bisa gayyatar da firaministan kasar Thailand Prayuth Chan-ocha ya yi, shugaba Xi zai isa birnin Bangkok na kasar, tsakanin ranar 17 zuwa 19 ga wata, don halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar hadin kan kasashen Asiya da yankin tekun Pasific a fannin tattalin arziki ko APEC karo na 29, wanda zai gudana a kasar Thailand, kana zai gudanar da ziyarar aiki a kasar.

  • Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Ana sa ran shugaba Xi zai gana da takwarorinsa na wasu kasashe, yayin ziyararsa ta wannan karo, wadanda suka hada da Emmanuel Macron na Faransa, da shugaba Joe Biden na kasar Amurka, da Macky Sall na kasar Senegal, da dai sauransu.

A yayin taron manema labaru da aka saba gudanarwa a wannan rana, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana fatan kasar Sin, game da halartar ayyukan da shugaba Xi Jinping zai gudanar.

Game da taron kolin G20 na tsibirin Bali, Zhao ya ce, wannan shi ne karo na farko da shugaban kasar Sin zai halarci taron koli na bangarori da dama, tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Ya ce a halin yanzu, duniya na fuskantar kalubale a fannin samun ci gaba, kuma a matsayinsa na babban dandalin hadin gwiwar tattalin arziki na kasa da kasa, ya kamata kungiyar G20 ta karfafa hadin kai, tare da daidaita manufofin tattalin arziki, da yin kokari tare, don neman dauwamamman ci gaban tattalin arzikin duniya yadda ya kamata.

Game da kwarya-kwaryar taron kolin na APEC, Zhao ya ce, APEC wani muhimmin dandali ne na hadin gwiwar tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasifik. Kuma shugaba Xi Jinping zai gabatar da muhimmin jawabi a gun taron, inda zai yi cikakken bayani kan muhimman manufofin kasar Sin, game da zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Asiya da tekun Pasifik, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin yanki da na duniya baki daya.

Zhao ya kara da cewa, “Muna sa ran dukkan bangarorin za su amince da ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Asiya da tekun Pacific, tare da sanya sabon kuzari ga ci gaban tattalin arzikin yankin, har ma da dukkanin duniya.” (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kubutar Da Mutane 3 Da Aka Sace, Sun Kwato AK-47 5 Da Babura 30 A Zamfara

Next Post

Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

16 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

17 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

18 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

19 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

20 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

21 hours ago
Next Post
Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.