• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin G20 Da Na APEC Tare Kuma Da Ziyara A Thailand
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying, ta sanar a yau Jumma’a cewa, bisa gayyatar da takwaransa na kasar Indonesiya Joko Widodo ya yi masa, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai isa tsibirin Bali na kasar Indonesiya, don halartar taron kolin kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki na G20 karo na 17, wanda zai gudana daga ranar 14 zuwa 17 ga watan da muke ciki.

Haka kuma, bisa gayyatar da firaministan kasar Thailand Prayuth Chan-ocha ya yi, shugaba Xi zai isa birnin Bangkok na kasar, tsakanin ranar 17 zuwa 19 ga wata, don halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar hadin kan kasashen Asiya da yankin tekun Pasific a fannin tattalin arziki ko APEC karo na 29, wanda zai gudana a kasar Thailand, kana zai gudanar da ziyarar aiki a kasar.

  • Kasar Sin Tana Goyon Bayan Bukatar Kasashe Masu Tasowa Game Da Kudaden Tallafin Sauyin Yanayi

Ana sa ran shugaba Xi zai gana da takwarorinsa na wasu kasashe, yayin ziyararsa ta wannan karo, wadanda suka hada da Emmanuel Macron na Faransa, da shugaba Joe Biden na kasar Amurka, da Macky Sall na kasar Senegal, da dai sauransu.

A yayin taron manema labaru da aka saba gudanarwa a wannan rana, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana fatan kasar Sin, game da halartar ayyukan da shugaba Xi Jinping zai gudanar.

Game da taron kolin G20 na tsibirin Bali, Zhao ya ce, wannan shi ne karo na farko da shugaban kasar Sin zai halarci taron koli na bangarori da dama, tun bayan babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20.

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Ya ce a halin yanzu, duniya na fuskantar kalubale a fannin samun ci gaba, kuma a matsayinsa na babban dandalin hadin gwiwar tattalin arziki na kasa da kasa, ya kamata kungiyar G20 ta karfafa hadin kai, tare da daidaita manufofin tattalin arziki, da yin kokari tare, don neman dauwamamman ci gaban tattalin arzikin duniya yadda ya kamata.

Game da kwarya-kwaryar taron kolin na APEC, Zhao ya ce, APEC wani muhimmin dandali ne na hadin gwiwar tattalin arziki a yankin Asiya da tekun Pasifik. Kuma shugaba Xi Jinping zai gabatar da muhimmin jawabi a gun taron, inda zai yi cikakken bayani kan muhimman manufofin kasar Sin, game da zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Asiya da tekun Pasifik, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin yanki da na duniya baki daya.

Zhao ya kara da cewa, “Muna sa ran dukkan bangarorin za su amince da ra’ayin gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga Asiya da tekun Pacific, tare da sanya sabon kuzari ga ci gaban tattalin arzikin yankin, har ma da dukkanin duniya.” (Mai fassara: Bilkisu Xin)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kubutar Da Mutane 3 Da Aka Sace, Sun Kwato AK-47 5 Da Babura 30 A Zamfara

Next Post

Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

Related

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

8 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

9 hours ago
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

10 hours ago
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

10 hours ago
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

11 hours ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

12 hours ago
Next Post
Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

Matakai 20 Na Kandagarki Da Shawo Kan Cutar COVID-19 Za Su Inganta Zirga-zirgar Al’umma Da Zuba Jari A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.