• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana a yau Juma’a da firaministan Girka, Kyriakos Mitsotakis a birnin Beijing. Yayin ganawar, shugaba Xi ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu cikin sama da rabin karni, Sin da Girka sun yi ta raya dangantakar cikin aminci da juriya.

Ya ce, a shirye Sin take ta inganta hadin gwiwar dabarun ci gaba da Girka, da zurfafa hadin gwiwa a fannonin sufuri da jiragen ruwa da makamashi da sadarwa da hada-hadar kudi da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannin bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” tare da samar da gaba mai karko da dorewa na tashar ruwa ta Piraeus

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

A nasa bangare, Kyriakos Mitsotakis ya ce, a shirye kasarsa take ta ci gaba da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin, da kara ci gajiya da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannonin jiragen ruwa da sufurin jiragen ruwa da makamashi mai tsafta, tana mai fatan karin kayayyakin kasar za su shiga kasuwar kasar Sin tare da maraba da masu yawon bude ido na Sin a Girka.

Sannan, shugaba Xi Jinping ya kuma gana da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz yau Juma’a ta kafar bidiyo.

Xi
Shugaba Xi da Takwaransa na Girka

A cewar Xi Jinping, a yanzu haka, cinikayya tsakanin Sin da Jamus na samun ci gaba yadda ya kamata, kuma yawan jari a tsakaninsu ma na karuwa, baya ga dangantakarsu dake kara kyautatuwa da kara karfi da samun nasarori.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Sama da kamfanonin Jamus 130 ne za su halarci baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin CIIE karo na 6, wanda ke nuna kwarin gwiwar da kamfanonin Jamus din ke da shi kan ci gaban Sin. Ana kuma fatan bangaren Jamus zai nace ga fadada bude kofar hadin gwiwa ga kamfanonin kasar Sin.

A nasa bangare, Olaf Scholz ya bayyana ra’ayin kasarsa game da rikicin Palasdinu da Isra’ila, yana mai fatan ci gaba da tuntubar juna tsakanin Jamus da Sin kan batun.

Game da hakan, Xi Jinping ya ce idan ana son warware tushen rikicin Palasdinu da Isra’ila ko kuma rikicin Ukraine, to akwai bukatar yin tunani mai zurfi a bangaren tsaro, da nacewa ga samar da cikakken tsaro na bai daya cikin hadin gwiwa da samar da ingantaccen tsarin tsaro mai dorewa kuma bisa adalci. (Fa’iza Mustapha)

(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGirkaJamus
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Next Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

3 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

5 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

5 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

8 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Next Post
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.