• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana a yau Juma’a da firaministan Girka, Kyriakos Mitsotakis a birnin Beijing. Yayin ganawar, shugaba Xi ya ce, tun bayan kulla huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu cikin sama da rabin karni, Sin da Girka sun yi ta raya dangantakar cikin aminci da juriya.

Ya ce, a shirye Sin take ta inganta hadin gwiwar dabarun ci gaba da Girka, da zurfafa hadin gwiwa a fannonin sufuri da jiragen ruwa da makamashi da sadarwa da hada-hadar kudi da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannin bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” tare da samar da gaba mai karko da dorewa na tashar ruwa ta Piraeus

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka
  • Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

A nasa bangare, Kyriakos Mitsotakis ya ce, a shirye kasarsa take ta ci gaba da inganta hadin gwiwar shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” da kasar Sin, da kara ci gajiya da fadada damarmakin hadin gwiwa a fannonin jiragen ruwa da sufurin jiragen ruwa da makamashi mai tsafta, tana mai fatan karin kayayyakin kasar za su shiga kasuwar kasar Sin tare da maraba da masu yawon bude ido na Sin a Girka.

Sannan, shugaba Xi Jinping ya kuma gana da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz yau Juma’a ta kafar bidiyo.

Xi
Shugaba Xi da Takwaransa na Girka

A cewar Xi Jinping, a yanzu haka, cinikayya tsakanin Sin da Jamus na samun ci gaba yadda ya kamata, kuma yawan jari a tsakaninsu ma na karuwa, baya ga dangantakarsu dake kara kyautatuwa da kara karfi da samun nasarori.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Sama da kamfanonin Jamus 130 ne za su halarci baje kolin kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin CIIE karo na 6, wanda ke nuna kwarin gwiwar da kamfanonin Jamus din ke da shi kan ci gaban Sin. Ana kuma fatan bangaren Jamus zai nace ga fadada bude kofar hadin gwiwa ga kamfanonin kasar Sin.

A nasa bangare, Olaf Scholz ya bayyana ra’ayin kasarsa game da rikicin Palasdinu da Isra’ila, yana mai fatan ci gaba da tuntubar juna tsakanin Jamus da Sin kan batun.

Game da hakan, Xi Jinping ya ce idan ana son warware tushen rikicin Palasdinu da Isra’ila ko kuma rikicin Ukraine, to akwai bukatar yin tunani mai zurfi a bangaren tsaro, da nacewa ga samar da cikakken tsaro na bai daya cikin hadin gwiwa da samar da ingantaccen tsarin tsaro mai dorewa kuma bisa adalci. (Fa’iza Mustapha)

(Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGirkaJamus
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Next Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

8 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

10 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

11 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

12 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

13 hours ago
Next Post
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cin Zarafin Shugabanta, Ajaero

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.