• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi

Yau Labara, an gudanar da taron kolin dandalin hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “Ziri daya da hanya daya” BRF karo na uku a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Babban sakataren kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana shugaban kasar, shugaban rundunar sojin kasar kasar Sin, Xi Jinping ya halarci bikin bude taron, tare da gabatar da jawabi.

A yayin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da sanarwar ayyuka 8 da kasar Sin za ta gudanar don tallafawa hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya” wato BRI mai inganci, ciki har da shimfida hanyar sadarwa mai alaka da hadin gwiwa mai bangarori uku na shawarar “ziri daya da hanya daya”, da goyon bayan raya tattalin arzikin duniya mai bin salon bude kofa, da aiwatar da hadin gwiwa mai inganci, da inganta samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da inganta kimiyya da fasaha, da inganta mu’amala tsakanin jama’a, da raya hanya ba tare da cin hanci da rashawa, da kuma inganta hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya”.

  • Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka

Haka kuma, Xi Jinping ya ce, cikin shekaru 10 da suka gabata, mun tsaya tsayin daka da yin hadin gwiwa domin inganta shawarar “Ziri daya da hanya daya”, wato BRI a takaice, inda hadin gwiwar dake tsakanin kasashen da abin ya shafa, ya bunkasa cikin sauri, har aka kai ga cimma dimbin sakamako masu gamsarwa.

Ya ce, cikin wadannan shekaru 10 ke nan, mun habaka hadin gwiwar kasashen duniya ta hanyoyin kasa, da na teku, da na sama, da ma hanyoyin sadarwa. Matakan da suka taka muhimmiya rawa wajen karfafa mu’amalar hajoji, da kudade, da fasahohi, da masana a tsakanin kasashen duniya, lamarin da ya kai ga bude sabon babin habaka hanyar siliki a sabon zamani.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, ana mai da hankali kan hadin gwiwa wajen habaka shawarar “ziri daya da hanya daya”, domin hadin gwiwa da taimakawa juna muhimman hanyoyi ne na samun dauwamammen ci gaba na shawarar. Muna son kafa dangantakar cude-ni-in-cude-ka, da aiwatar da ka’idojin yin mu’amala da juna da cimma moriyar juna, ta yadda za a samu ci gaba tare, da cimma nasarori cikin hadin gwiwa.
Bugu da kari, ya ce, ba za mu nuna adawa kan bambancin al’adu ba, kuma, ba za mu yi gasar siyasa bisa yankunan da muke ciki ba, balle ma yakin siyasa a tsakanin kawance daban daban. Kasar Sin tana adawa da takunkumin rashin adalci, da kalubalen tattalin arziki, kuma ba ta son dakile huldar ciniki dake tsakaninta da sauran kasashen duniya.
Ya kara da cewa, mun gane cewa, dukkanin bil Adama na da makomar bai daya, idan babu bunkasuwar kasashen duniya, ba za a sami bunkasuwar kasar Sin ba, kana, idan kasar Sin ta bunkasa kamar yadda ake fata, tabbas kasashen duniya za su sami karin bunkasuwa.

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Shugaba Xi ya jaddada cewa, wadannan shekaru 10 da suka gabata sun nuna mana cewa, inganta shawarar “ziri daya da hanya daya” cikin hadin gwiwa, ya kasance abu mafi dacewa da muka yi, ya kuma dace da halin da muke ciki. Ya kamata mu sauke nauyin da ke kanmu yadda ya kamata domin kare tarihin bil Adama, da kiyaye al’umma, tare da raya duniyarmu, haka kuma, ya dace mu hada kanmu wajen fuskantar kalubalolin dake gabanmu, ta yadda za a samar da wata makoma mai haske ga ’ya’yanmu da jikokinmu. (Mai Fassarawa: Safiyah Ma&Maryam Yang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26
Daga Birnin Sin

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Next Post
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Majalisa Ta Nemi Jami'an Tsaro Su Ceto Daliban Jami'ar Gusau 30 Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.