• English
  • Business News
Friday, June 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Sanar Da Matakai 8 Na Tallafawa Raya Hadin Gwiwar Shawarar BRI Mai Inganci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Labara, an gudanar da taron kolin dandalin hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “Ziri daya da hanya daya” BRF karo na uku a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin. Babban sakataren kwamitin tsakiyar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin, kana shugaban kasar, shugaban rundunar sojin kasar kasar Sin, Xi Jinping ya halarci bikin bude taron, tare da gabatar da jawabi.

A yayin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da sanarwar ayyuka 8 da kasar Sin za ta gudanar don tallafawa hadin gwiwar shawarar “ziri daya da hanya daya” wato BRI mai inganci, ciki har da shimfida hanyar sadarwa mai alaka da hadin gwiwa mai bangarori uku na shawarar “ziri daya da hanya daya”, da goyon bayan raya tattalin arzikin duniya mai bin salon bude kofa, da aiwatar da hadin gwiwa mai inganci, da inganta samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da inganta kimiyya da fasaha, da inganta mu’amala tsakanin jama’a, da raya hanya ba tare da cin hanci da rashawa, da kuma inganta hadin gwiwar kasa da kasa kan shawarar “ziri daya da hanya daya”.

  • Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka

Haka kuma, Xi Jinping ya ce, cikin shekaru 10 da suka gabata, mun tsaya tsayin daka da yin hadin gwiwa domin inganta shawarar “Ziri daya da hanya daya”, wato BRI a takaice, inda hadin gwiwar dake tsakanin kasashen da abin ya shafa, ya bunkasa cikin sauri, har aka kai ga cimma dimbin sakamako masu gamsarwa.

Ya ce, cikin wadannan shekaru 10 ke nan, mun habaka hadin gwiwar kasashen duniya ta hanyoyin kasa, da na teku, da na sama, da ma hanyoyin sadarwa. Matakan da suka taka muhimmiya rawa wajen karfafa mu’amalar hajoji, da kudade, da fasahohi, da masana a tsakanin kasashen duniya, lamarin da ya kai ga bude sabon babin habaka hanyar siliki a sabon zamani.

Shugaba Xi ya jaddada cewa, ana mai da hankali kan hadin gwiwa wajen habaka shawarar “ziri daya da hanya daya”, domin hadin gwiwa da taimakawa juna muhimman hanyoyi ne na samun dauwamammen ci gaba na shawarar. Muna son kafa dangantakar cude-ni-in-cude-ka, da aiwatar da ka’idojin yin mu’amala da juna da cimma moriyar juna, ta yadda za a samu ci gaba tare, da cimma nasarori cikin hadin gwiwa.
Bugu da kari, ya ce, ba za mu nuna adawa kan bambancin al’adu ba, kuma, ba za mu yi gasar siyasa bisa yankunan da muke ciki ba, balle ma yakin siyasa a tsakanin kawance daban daban. Kasar Sin tana adawa da takunkumin rashin adalci, da kalubalen tattalin arziki, kuma ba ta son dakile huldar ciniki dake tsakaninta da sauran kasashen duniya.
Ya kara da cewa, mun gane cewa, dukkanin bil Adama na da makomar bai daya, idan babu bunkasuwar kasashen duniya, ba za a sami bunkasuwar kasar Sin ba, kana, idan kasar Sin ta bunkasa kamar yadda ake fata, tabbas kasashen duniya za su sami karin bunkasuwa.

Labarai Masu Nasaba

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

Shugaba Xi ya jaddada cewa, wadannan shekaru 10 da suka gabata sun nuna mana cewa, inganta shawarar “ziri daya da hanya daya” cikin hadin gwiwa, ya kasance abu mafi dacewa da muka yi, ya kuma dace da halin da muke ciki. Ya kamata mu sauke nauyin da ke kanmu yadda ya kamata domin kare tarihin bil Adama, da kiyaye al’umma, tare da raya duniyarmu, haka kuma, ya dace mu hada kanmu wajen fuskantar kalubalolin dake gabanmu, ta yadda za a samar da wata makoma mai haske ga ’ya’yanmu da jikokinmu. (Mai Fassarawa: Safiyah Ma&Maryam Yang)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BRTShawarar ziri dayaSunTaroXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Jarida Sun Cancanci Samun Rayuwa Mai Inganci A Nijeriya – Minista

Next Post

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Related

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
Daga Birnin Sin

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

2 hours ago
Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

3 hours ago
Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55
Daga Birnin Sin

Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

3 hours ago
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
Daga Birnin Sin

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

3 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

5 hours ago
Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
Daga Birnin Sin

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

7 hours ago
Next Post
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Majalisa Ta Nemi Jami'an Tsaro Su Ceto Daliban Jami'ar Gusau 30 Da Aka Sace

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

June 12, 2025
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025

June 12, 2025
Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

Sin Na Fatan Amurka Ta Yi Hadin Gwiwa Da Ita Don Tabbatar Da Matsayar Da Shugabannin Kasashen Biyu Suka Cimma

June 12, 2025
Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

Sin Ta sanya Indonesiya Cikin Tsarin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Na Sa’o’i 240 Da Kara Yawan Kasashen Tsarin Zuwa 55

June 12, 2025
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka

June 12, 2025
Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

June 12, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 

June 12, 2025
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

June 12, 2025
Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

June 12, 2025
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

June 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.