• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Sanar Da Matakan Kara Bude Kofa A Fannin Samar Da Hidimomi Yayin Bude Baje Kolin CIFTIS Na 2023

by CMG Hausa
2 years ago
Sin

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ce kasar sa za ta kara bude kofofin ta a fannonin ba da hidimomi, wadanda suka hada da na fasahar sadarwar wayar tarho, da yawon bude ido, da jarrabawa a bangarorin shari’a da ilimin koyar da sana’o’i.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne a Asabar din nan, yayin da yake jawabi ta kafar bidiyo ga taron baje kolin kasa da kasa na kasar Sin na shekarar 2023, game da hada hadar cinikayyar ba da hidima ko CIFTIS.

Xi ya ce domin bunkasa damar ci gaba a fannin kara bude kofofin kasar Sin, ta yadda kowa zai iya shiga a dama da shi, Sin za ta fadada damammakin kasa da kasa na inganta yankunan cinikayya maras shinge, za ta kuma shiga a dama da ita wajen gudanar da shawarwarin shawo kan mummunan tasirin dake akwai, don gane da sassan ba da hidima da na zuba jari da ake kayyadewa.

Kaza lika, shugaban na Sin ya ce babban hadadden yankin gwaji domin bude kofa a fannonin ba da hidima na Sin, da yankunan cinikayya maras shinge na gwaji, da tashoshin ruwa na gudanar da cinikayya maras shinge, su ne za su fara daidaita manufofin su, ta yadda za su yi kafada da kafada da managartan dokokin raya tattalin arziki, da cinikayya na kasa da kasa.

Bikin baje kolin na bana dai na da taken “Bude kofa na haifar da ci gaba, yin hadin gwiwa na inganta makoma”. Zai kuma gudana tsakanin Asabar din nan zuwa ranar Larabar makon gobe. Kaza lika yayin baje kolin na wannan lokaci za a gudanar da sama da ayyuka 200, ciki har da dandaloli, da shawarwari, da tarukan karawa juna sani.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Bikin na bana ya samu halartar kasashe, da hukumomin kasa da kasa 83, yayin da kuma manyan kamfanoni da cibiyoyi sama da 70 ke baje nasarorin su, kana akwai sama da kamfanoni 2,400 dake halartar baje kolin a zahiri. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Next Post
Haaland Ya Jefa Kwallo Uku Rigis A Ragar Fulham

Haaland Ya Jefa Kwallo Uku Rigis A Ragar Fulham

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.