• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Indonesia

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Xi Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Indonesia
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gana da takwaransa na kasar Indonesia Joko Widodo da ke ziyara a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Xi ya yi nuni da cewa, a karkashin jagorancin hadin gwiwarmu, dangantakar dake tsakanin Sin da Indonesia ta bunkasa cikin ‘yan shekarun nan, inda ta nuna juriya da kuzari.

  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Nace Kan Ra’ayin Hadin Gwiwa Na Hakika A Taron G20 A Indonesia

Bangarorin biyu sun karfafa amincewa da juna bisa manyan tsare-tsare da zurfafa hadin gwiwar siyasa, da tattalin arziki, da al’adu da na harkokin teku.

Haka kuma, kasashen suna nuna irin nauyin da ke bisa wuyansu, tare da samun nasarori masu gamsarwa wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, da inganta nuna goyon baya da hadin gwiwa a duniya, da nuna kyakkyawan misali ga manyan kasashe masu tasowa, wajen neman karfi ta hanyar hadin kai da cin moriyar juna.

Shugaba Xi ya ce, ya kamata bangarorin biyu su zurfafa hadin gwiwa mai inganci game da shawarar “ziri daya da hanya daya” da samar da karin sakamako.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Xi ya yi nuni da cewa, sauye-sauyen da ake fuskanta a duniya, suna bulla ta hanyoyin da ba a taba ganin irinsu ba.

Don haka, ya kamata kasashen Sin da Indonesia, su yi aiki tare don nuna nauyin da ke bisa wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe masu tasowa, da aiwatar da ra’ayin bangarori daban-daban na zahiri, da kiyaye bude kofa ga kasashen waje, da ba da hikimomi na kasashen dake gabashin duniya, da ba da gudummawar karfin Asiya wajen tafiyar da harkokin kasa da kasa.

A nasa jawabin kuwa, Joko Widodo ya bayyana cewa, kasashen Indonesia da Sin, abokan hulda ne bisa manyan tsare-tsare, kuma sun tsara muhimmin buri na gina al’umma mai makoma ta bai daya.

Hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu, ta cin moriyar juna da samun nasara tare ce, wanda ba wai kawai tana kawo alfanu ga al’ummomin kasashen biyu ba, har ma tana bayar da muhimmiyar gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaba a shiyyar da ma duniya baki daya.

Ya kara da cewa, kasar Indonesia tana son yin aiki tare da kasar Sin, don ci gaba da zurfafa hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen biyu, da ba da babbar gudummawa ga zaman lafiya a yankin da ci gaban duk duniya.(Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Next Post

Majalisa Ta Musanta Shirin Tsige Kakakin Majalisar, Femi Gbajabiamila

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

2 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

3 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

5 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

8 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

9 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

10 hours ago
Next Post
Majalisa Ta Musanta Shirin Tsige Kakakin Majalisar, Femi Gbajabiamila

Majalisa Ta Musanta Shirin Tsige Kakakin Majalisar, Femi Gbajabiamila

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.