• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

by CMG Hausa
2 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da hanzarta fadada tsarin BRICS, da kara kokarin tabbatar da tafiyar da harkokin duniya bisa adalci.

Xi ya bayyana hakan ne, Larabar nan a yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron kolin kasashen BRICS karo na 15. Ya kuma bayyana cewa, ci gaba wani hakki ne da ba a za a iya tauyewa dukkan kasashe ba, kuma ba wata dama ce ta wasu kasashe kalilan ba. Ya kamata kowa ya rubuta kuma ya kiyaye ka’idojin kasa da kasa kamar yadda kundin tsarin MDD ya tanada, kuma ba za a lamunci sanya dokokin cikin gida a matsayin ka’idojin kasa da kasa ba.

  • CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Ban da haka kuma, shugaba Xi ya ce, kasar Sin za ta kafa wani rukunin kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na Sin da BRICS na sabon zamani, yayin da kasashen BRICS suka amince da kaddamar da rukunin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan-Adam (AI) da fadada hadin gwiwar fasahar ta AI.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a aiwatar da manufar nan ta gina al’umma mai makomar bai daya ga daukanin bil adama a zahiri. Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya Talata a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu, cikin jawabinsa, da ministan ma’aikatar cinikayyar kasar Sin Wang Wentao ya karanta, yayin zaman dandalin kasuwanci na taron BRICS dake gudana yanzu haka.

A cikin jawabin mai taken “Inganta goyon baya da hadin gwiwa domin shawo kan hadurra da kalubale, da hada karfi wajen gina duniya mai karko”, shugaban na Sin ya ce “Ya kamata mu ingiza ci gaba da walwalar kowa da kowa. Akwai bukatar cimma yanayin tsaron duniya na bai daya, da kara zage damtse wajen yin musaya tsakanin mabanbantan wayewar kai, da yin koyi da juna”. Kaza lika shugaba Xi ya ce yunkurowar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da kasashe masu tasowa, wanda kungiyar BRICS ke wakilta, ya yi matukar sauya alkiblar duniya, kuma duk wata turjiya da za a iya fuskanta, ba za ta hana BRICS mai karfi da inganci ci gaba da bunkasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

Har ila yau, Xi ya ce Sin na neman bunkasuwa ta bai daya tare da sauran kasashe masu tasowa, tana kuma martaba moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa, kana tana aiki tukuru wajen kara fadada wakilci, da karfin muryar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da takwarorin su kasashe masu tasowa a harkokin kasa da kasa.

Bugu da kari, Sin za ta ci gaba da zama muhimmiyar dama ga ci gaban duniya. A hannu guda kuma, za ta tsaya tsayin daka wajen ingiza matakan bude kofofin ta, da goyon bayan barin kasuwa ta yi halin ta bisa kyakkyawan yanayi, wanda ya yi daidai da tsarin dokoki na adalci, da kuma gina cudanyar yankunan kasuwanci maras shinge tsakanin kasa da kasa, wanda dukkanin sassa za su amincewa. (Masu Fassara: Saminu Hassan, Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
Next Post
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

LABARAI MASU NASABA

Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.