• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

byCMG Hausa
2 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da hanzarta fadada tsarin BRICS, da kara kokarin tabbatar da tafiyar da harkokin duniya bisa adalci.

Xi ya bayyana hakan ne, Larabar nan a yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron kolin kasashen BRICS karo na 15. Ya kuma bayyana cewa, ci gaba wani hakki ne da ba a za a iya tauyewa dukkan kasashe ba, kuma ba wata dama ce ta wasu kasashe kalilan ba. Ya kamata kowa ya rubuta kuma ya kiyaye ka’idojin kasa da kasa kamar yadda kundin tsarin MDD ya tanada, kuma ba za a lamunci sanya dokokin cikin gida a matsayin ka’idojin kasa da kasa ba.

  • CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Ban da haka kuma, shugaba Xi ya ce, kasar Sin za ta kafa wani rukunin kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na Sin da BRICS na sabon zamani, yayin da kasashen BRICS suka amince da kaddamar da rukunin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan-Adam (AI) da fadada hadin gwiwar fasahar ta AI.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a aiwatar da manufar nan ta gina al’umma mai makomar bai daya ga daukanin bil adama a zahiri. Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya Talata a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu, cikin jawabinsa, da ministan ma’aikatar cinikayyar kasar Sin Wang Wentao ya karanta, yayin zaman dandalin kasuwanci na taron BRICS dake gudana yanzu haka.

A cikin jawabin mai taken “Inganta goyon baya da hadin gwiwa domin shawo kan hadurra da kalubale, da hada karfi wajen gina duniya mai karko”, shugaban na Sin ya ce “Ya kamata mu ingiza ci gaba da walwalar kowa da kowa. Akwai bukatar cimma yanayin tsaron duniya na bai daya, da kara zage damtse wajen yin musaya tsakanin mabanbantan wayewar kai, da yin koyi da juna”. Kaza lika shugaba Xi ya ce yunkurowar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da kasashe masu tasowa, wanda kungiyar BRICS ke wakilta, ya yi matukar sauya alkiblar duniya, kuma duk wata turjiya da za a iya fuskanta, ba za ta hana BRICS mai karfi da inganci ci gaba da bunkasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Har ila yau, Xi ya ce Sin na neman bunkasuwa ta bai daya tare da sauran kasashe masu tasowa, tana kuma martaba moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa, kana tana aiki tukuru wajen kara fadada wakilci, da karfin muryar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da takwarorin su kasashe masu tasowa a harkokin kasa da kasa.

Bugu da kari, Sin za ta ci gaba da zama muhimmiyar dama ga ci gaban duniya. A hannu guda kuma, za ta tsaya tsayin daka wajen ingiza matakan bude kofofin ta, da goyon bayan barin kasuwa ta yi halin ta bisa kyakkyawan yanayi, wanda ya yi daidai da tsarin dokoki na adalci, da kuma gina cudanyar yankunan kasuwanci maras shinge tsakanin kasa da kasa, wanda dukkanin sassa za su amincewa. (Masu Fassara: Saminu Hassan, Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version