ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

by CMG Hausa
3 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da hanzarta fadada tsarin BRICS, da kara kokarin tabbatar da tafiyar da harkokin duniya bisa adalci.

Xi ya bayyana hakan ne, Larabar nan a yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron kolin kasashen BRICS karo na 15. Ya kuma bayyana cewa, ci gaba wani hakki ne da ba a za a iya tauyewa dukkan kasashe ba, kuma ba wata dama ce ta wasu kasashe kalilan ba. Ya kamata kowa ya rubuta kuma ya kiyaye ka’idojin kasa da kasa kamar yadda kundin tsarin MDD ya tanada, kuma ba za a lamunci sanya dokokin cikin gida a matsayin ka’idojin kasa da kasa ba.

  • CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Ban da haka kuma, shugaba Xi ya ce, kasar Sin za ta kafa wani rukunin kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na Sin da BRICS na sabon zamani, yayin da kasashen BRICS suka amince da kaddamar da rukunin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan-Adam (AI) da fadada hadin gwiwar fasahar ta AI.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a aiwatar da manufar nan ta gina al’umma mai makomar bai daya ga daukanin bil adama a zahiri. Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya Talata a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu, cikin jawabinsa, da ministan ma’aikatar cinikayyar kasar Sin Wang Wentao ya karanta, yayin zaman dandalin kasuwanci na taron BRICS dake gudana yanzu haka.

A cikin jawabin mai taken “Inganta goyon baya da hadin gwiwa domin shawo kan hadurra da kalubale, da hada karfi wajen gina duniya mai karko”, shugaban na Sin ya ce “Ya kamata mu ingiza ci gaba da walwalar kowa da kowa. Akwai bukatar cimma yanayin tsaron duniya na bai daya, da kara zage damtse wajen yin musaya tsakanin mabanbantan wayewar kai, da yin koyi da juna”. Kaza lika shugaba Xi ya ce yunkurowar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da kasashe masu tasowa, wanda kungiyar BRICS ke wakilta, ya yi matukar sauya alkiblar duniya, kuma duk wata turjiya da za a iya fuskanta, ba za ta hana BRICS mai karfi da inganci ci gaba da bunkasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Har ila yau, Xi ya ce Sin na neman bunkasuwa ta bai daya tare da sauran kasashe masu tasowa, tana kuma martaba moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa, kana tana aiki tukuru wajen kara fadada wakilci, da karfin muryar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da takwarorin su kasashe masu tasowa a harkokin kasa da kasa.

Bugu da kari, Sin za ta ci gaba da zama muhimmiyar dama ga ci gaban duniya. A hannu guda kuma, za ta tsaya tsayin daka wajen ingiza matakan bude kofofin ta, da goyon bayan barin kasuwa ta yi halin ta bisa kyakkyawan yanayi, wanda ya yi daidai da tsarin dokoki na adalci, da kuma gina cudanyar yankunan kasuwanci maras shinge tsakanin kasa da kasa, wanda dukkanin sassa za su amincewa. (Masu Fassara: Saminu Hassan, Ibrahim Yaya)

Xi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.