ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Ya Yi Kira Da Hanzarta Fadada BRICS Da Kuma Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Daukacin Bil Adama A Zahiri

by CMG Hausa
3 years ago
Xi

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da hanzarta fadada tsarin BRICS, da kara kokarin tabbatar da tafiyar da harkokin duniya bisa adalci.

Xi ya bayyana hakan ne, Larabar nan a yayin da yake gabatar da jawabi a wajen taron kolin kasashen BRICS karo na 15. Ya kuma bayyana cewa, ci gaba wani hakki ne da ba a za a iya tauyewa dukkan kasashe ba, kuma ba wata dama ce ta wasu kasashe kalilan ba. Ya kamata kowa ya rubuta kuma ya kiyaye ka’idojin kasa da kasa kamar yadda kundin tsarin MDD ya tanada, kuma ba za a lamunci sanya dokokin cikin gida a matsayin ka’idojin kasa da kasa ba.

  • CMG Da Kafofin Watsa Labaran Afirka Sun Kulla Sabuwar Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Ban da haka kuma, shugaba Xi ya ce, kasar Sin za ta kafa wani rukunin kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na Sin da BRICS na sabon zamani, yayin da kasashen BRICS suka amince da kaddamar da rukunin nazarin fasahar kwaikwayon tunanin dan-Adam (AI) da fadada hadin gwiwar fasahar ta AI.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a aiwatar da manufar nan ta gina al’umma mai makomar bai daya ga daukanin bil adama a zahiri. Shugaban ya yi wannan kira ne a jiya Talata a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu, cikin jawabinsa, da ministan ma’aikatar cinikayyar kasar Sin Wang Wentao ya karanta, yayin zaman dandalin kasuwanci na taron BRICS dake gudana yanzu haka.

A cikin jawabin mai taken “Inganta goyon baya da hadin gwiwa domin shawo kan hadurra da kalubale, da hada karfi wajen gina duniya mai karko”, shugaban na Sin ya ce “Ya kamata mu ingiza ci gaba da walwalar kowa da kowa. Akwai bukatar cimma yanayin tsaron duniya na bai daya, da kara zage damtse wajen yin musaya tsakanin mabanbantan wayewar kai, da yin koyi da juna”. Kaza lika shugaba Xi ya ce yunkurowar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da kasashe masu tasowa, wanda kungiyar BRICS ke wakilta, ya yi matukar sauya alkiblar duniya, kuma duk wata turjiya da za a iya fuskanta, ba za ta hana BRICS mai karfi da inganci ci gaba da bunkasa ba.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Har ila yau, Xi ya ce Sin na neman bunkasuwa ta bai daya tare da sauran kasashe masu tasowa, tana kuma martaba moriyar bai daya ta kasashe masu tasowa, kana tana aiki tukuru wajen kara fadada wakilci, da karfin muryar kasashe masu saurin bunkasar tattalin arziki, da takwarorin su kasashe masu tasowa a harkokin kasa da kasa.

Bugu da kari, Sin za ta ci gaba da zama muhimmiyar dama ga ci gaban duniya. A hannu guda kuma, za ta tsaya tsayin daka wajen ingiza matakan bude kofofin ta, da goyon bayan barin kasuwa ta yi halin ta bisa kyakkyawan yanayi, wanda ya yi daidai da tsarin dokoki na adalci, da kuma gina cudanyar yankunan kasuwanci maras shinge tsakanin kasa da kasa, wanda dukkanin sassa za su amincewa. (Masu Fassara: Saminu Hassan, Ibrahim Yaya)

Xi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

Dole ne Japan Ta Dakatar Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Bin Wata Hanya Mafi Dacewa

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.