• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xinjiang Ta Soki Matsayar Amurka Ta Sanya Wani Kamfanin Fasaha Cikin Jerin Kamfanonin Da Ta Kakabawa Takunkumi

by CMG Hausa
3 years ago
Xinjiang

A ranar 15 ga watan nan na Disamba ne gwamnatin Amurka, ta kara wasu kamfanonin kasar Sin su 36, cikin jerin kamfanonin da ta sanyawa takunkumin shigar da hajojin su cikin Amurka, ciki har da kamfanin Tiandy Technologies, wanda Amurkan ta zarga da aikata danniya, da taimakawa wajen tsare mutane, da leken sirrikan mutane ta amfani da fasahohin zamani, da keta hakkokin bil Adama, matakin da Amurka ta ce wai, ya shafi al’ummun Uygurs, da na Kazakhs, da sauran musulmin kananan kabilun dake sassan kasar ta Sin.

Kamfanin Tiandy Technologies mai hedkwata a birnin Tianjin, na samar da na’urorin sanya ido ne, yana kuma bayar da hidimomi masu nasaba da hakan. Yana kuma hada sassan fasahohin kwaikwayon tunanin bil Adama da fasahar tattara manyan bayanai, da fasahar ajiyar su, da sauran fasahohin yanar gizo, da na kyamarori, wajen samar da bayanai na tabbatar da tsaro.

  • Jawabin Shugaban Kasar Sin Na Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2023

Da yake tsokaci kan matakin gwamnatin Amurka kan wannan kamfani, kakakin gwamnatin jihar Xinjiang Xu Guixiang, ya ce kamfanin Tiandy Technologies yana da rajista bisa doka, kuma jihar Xinjiang na amfani da na’urorin sa ne wajen tattara bayanai, da inganta ayyukan jagorancin jihar, da gina al’umma mai yanayin zaman lafiya, ta yadda kowa zai rayu tare da gudanar da ayyuka cikin zaman lafiya da wadatuwa. Xu ya kara da cewa, kamfanin ba ya harin wasu rukunin kabilu ko gungun al’umma, kana ba shi da wani tarihi na keta hakkokin bil Adama, ta hanyar leken asiri ta amfani da manyan fasahohi.

Har ila yau, jami’in ya ce abu ne sananne a duniya, kasashe daban daban na amfani da na’urorin fasahohin zamani, a ayyukan jagorancin al’umma, kuma Amurka ita kan ta na kan gaba, wajen zuba jari, da bincike, da samar da hajoji da manhajoji na inganta tsaro, da tattara manyan bayanai, da samar da dandaloli na killace bayanai.

Don haka, abun tambaya a nan a cewar jami’in shi ne, shi ma wannan mataki na Amurka, na leken asirin Amurkawa ne? (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka
Daga Birnin Sin

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Za Ta Fadada Fitar  Da Zobo Zuwa Ketare

Gwamnatin Kano Za Ta Fadada Fitar  Da Zobo Zuwa Ketare

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.