• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi hasashen dalar Amurka na iya kaiwa Naira 1,000 a kasuwannin canjin kudin Nijeriya, lamarin dake kara jefa fargabar karuwar tsadar rayuwa a zukatan ’yan Nijeriya. Kwan-gaba-kwan-bayan farashin dalar Amurka a Nijeriya sama da shekara 20 da suka gabata ya dankwafar da darajar Naira.

Majiyoyi daban-daban daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa harkokin shigo da kaya daga waje sun dara na fitar da su yawa a kasar. Na fitarwa wanda da su ake samun dalar, ba su wuce kashi 8.83% ba, na shigarwa kuma kashi 16.57%, sun kusan ninkawa.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Kasashe da dama sun fara farkawa daga baccin rafkana domin yi wa kansu mafita a kan kangin dalar Amurka. Tuni Argentina, Brazil da Bolivia dake nahiyar kudancin Amurka suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancinsu da Sin. Abin yana kara samun tagomashi a yankin Latin da Caribbean.

Wajibi ne kasashe su samar wa kansu mafita don rage dogaro da dalar Amurka sakamakon karuwar kudaden ruwa a kan dalar da ramewar asusun ajiyarsu na waje. Masana tattalin arziki na nuna cewa za a samu kasashen duniya da dama da za su rungumi amfani da kudin Sin RMB wajen huldar kasuwanci saboda kasancewar Sin a matsayin kasa mafi girman hada-hadar kasuwanci a duniya. Ko a kwanan baya, an ruwaito shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva yana kiran kasashen duniya su samar wa kansu mafita a kan amfani da dalar Amurka, domin a cewarsa me ya sa dukkan kasashen duniya ke amfani da dalar a kasuwancinsu.

Bugu da kari, gwamnatocin kasashen waje da ke bukatar adana kudaden ajiyarsu na waje da dalar Amurka za su kara kashe kudi wajen neman dalar, inda lamarin zai fi shafar tattalin arzikin kasashe masu tasowa saboda ribar da ake samu wajen fitar da kaya zuwa waje ta ragu.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Haka zalika, Rasha da Sin sun cimma yarjejeniya don fara biyan kudin iskar gas da take samarwa kasar Sin a kudin Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Har ila yau, masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin mai ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Yayin da wannan yunkuri na fita daga kangin dalar Amurka ke samun tagomashi, Kasashe masu kawancen bunkasa ci gabansu na BRICS (Brazil, Rasha, Indiya, Sin, da Afirka ta Kudu) suna shirin kaddamar da sabon kudin da kasashe mambobin kungiyar za su rika amfani da su wajen cinikayya a tsakaninsu. Haka nan gabanin taron kolin kungiyar BRICS na watan Agusta da za a yi a Afirka ta Kudu, yanzu haka akwai kasashe 24 da ke neman kulla kawance domin fita daga tarnakin da dalar Amurka ta yi musu na tsawon shekaru. Kasashen sun hada da Najeriya, Saudi Arabiya, Iran, Argentina, Hadaddiyar Daular Larabawa, Aljeriya, Masar, Bahrain, Indonesia da wasu kasashe na Afirka.

Ko a ’yan watannin baya, Kenya ta sauwake wa kanta nemo Dala Miliyan 500 duk wata don biyan kudin fetur da take shigo da shi, sakamakon kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings.

Ya kamata Nijeriya ta dauki darasi ta farfado da yarjejeniyar musanyar kudin nan a tsakaninta da Sin ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 da aka kulla a 2018, saboda kasuwancin dake tsakaninsu wanda ko a watanni ukun farko na shekarar nan ya kai kimanin Naira Tiriliyan Hudu da Biliyan Hamsin da Biyar da Miliyan Dari Biyu da Talatin da Takwas (4,055,238,000.00), kamar yadda aka ruwaito Jami’ar Ofishin Jakadancin Sin a Legas, Ms. Yan Yuqing tana fada a ’yan watannin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisar Dokokin NijeriyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Bude Bikin Baje Kolin Cinikayyar Hidima Na 2023 A Satumba

Next Post

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

17 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

18 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

19 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

20 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

21 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.