• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Dalar Amurka

An yi hasashen dalar Amurka na iya kaiwa Naira 1,000 a kasuwannin canjin kudin Nijeriya, lamarin dake kara jefa fargabar karuwar tsadar rayuwa a zukatan ’yan Nijeriya. Kwan-gaba-kwan-bayan farashin dalar Amurka a Nijeriya sama da shekara 20 da suka gabata ya dankwafar da darajar Naira.

Majiyoyi daban-daban daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa harkokin shigo da kaya daga waje sun dara na fitar da su yawa a kasar. Na fitarwa wanda da su ake samun dalar, ba su wuce kashi 8.83% ba, na shigarwa kuma kashi 16.57%, sun kusan ninkawa.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Kasashe da dama sun fara farkawa daga baccin rafkana domin yi wa kansu mafita a kan kangin dalar Amurka. Tuni Argentina, Brazil da Bolivia dake nahiyar kudancin Amurka suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancinsu da Sin. Abin yana kara samun tagomashi a yankin Latin da Caribbean.

Wajibi ne kasashe su samar wa kansu mafita don rage dogaro da dalar Amurka sakamakon karuwar kudaden ruwa a kan dalar da ramewar asusun ajiyarsu na waje. Masana tattalin arziki na nuna cewa za a samu kasashen duniya da dama da za su rungumi amfani da kudin Sin RMB wajen huldar kasuwanci saboda kasancewar Sin a matsayin kasa mafi girman hada-hadar kasuwanci a duniya. Ko a kwanan baya, an ruwaito shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva yana kiran kasashen duniya su samar wa kansu mafita a kan amfani da dalar Amurka, domin a cewarsa me ya sa dukkan kasashen duniya ke amfani da dalar a kasuwancinsu.

Bugu da kari, gwamnatocin kasashen waje da ke bukatar adana kudaden ajiyarsu na waje da dalar Amurka za su kara kashe kudi wajen neman dalar, inda lamarin zai fi shafar tattalin arzikin kasashe masu tasowa saboda ribar da ake samu wajen fitar da kaya zuwa waje ta ragu.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Haka zalika, Rasha da Sin sun cimma yarjejeniya don fara biyan kudin iskar gas da take samarwa kasar Sin a kudin Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Har ila yau, masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin mai ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Yayin da wannan yunkuri na fita daga kangin dalar Amurka ke samun tagomashi, Kasashe masu kawancen bunkasa ci gabansu na BRICS (Brazil, Rasha, Indiya, Sin, da Afirka ta Kudu) suna shirin kaddamar da sabon kudin da kasashe mambobin kungiyar za su rika amfani da su wajen cinikayya a tsakaninsu. Haka nan gabanin taron kolin kungiyar BRICS na watan Agusta da za a yi a Afirka ta Kudu, yanzu haka akwai kasashe 24 da ke neman kulla kawance domin fita daga tarnakin da dalar Amurka ta yi musu na tsawon shekaru. Kasashen sun hada da Najeriya, Saudi Arabiya, Iran, Argentina, Hadaddiyar Daular Larabawa, Aljeriya, Masar, Bahrain, Indonesia da wasu kasashe na Afirka.

Ko a ’yan watannin baya, Kenya ta sauwake wa kanta nemo Dala Miliyan 500 duk wata don biyan kudin fetur da take shigo da shi, sakamakon kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings.

Ya kamata Nijeriya ta dauki darasi ta farfado da yarjejeniyar musanyar kudin nan a tsakaninta da Sin ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 da aka kulla a 2018, saboda kasuwancin dake tsakaninsu wanda ko a watanni ukun farko na shekarar nan ya kai kimanin Naira Tiriliyan Hudu da Biliyan Hamsin da Biyar da Miliyan Dari Biyu da Talatin da Takwas (4,055,238,000.00), kamar yadda aka ruwaito Jami’ar Ofishin Jakadancin Sin a Legas, Ms. Yan Yuqing tana fada a ’yan watannin baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Next Post
Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.