• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi hasashen dalar Amurka na iya kaiwa Naira 1,000 a kasuwannin canjin kudin Nijeriya, lamarin dake kara jefa fargabar karuwar tsadar rayuwa a zukatan ’yan Nijeriya. Kwan-gaba-kwan-bayan farashin dalar Amurka a Nijeriya sama da shekara 20 da suka gabata ya dankwafar da darajar Naira.

Majiyoyi daban-daban daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa harkokin shigo da kaya daga waje sun dara na fitar da su yawa a kasar. Na fitarwa wanda da su ake samun dalar, ba su wuce kashi 8.83% ba, na shigarwa kuma kashi 16.57%, sun kusan ninkawa.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Kasashe da dama sun fara farkawa daga baccin rafkana domin yi wa kansu mafita a kan kangin dalar Amurka. Tuni Argentina, Brazil da Bolivia dake nahiyar kudancin Amurka suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancinsu da Sin. Abin yana kara samun tagomashi a yankin Latin da Caribbean.

Wajibi ne kasashe su samar wa kansu mafita don rage dogaro da dalar Amurka sakamakon karuwar kudaden ruwa a kan dalar da ramewar asusun ajiyarsu na waje. Masana tattalin arziki na nuna cewa za a samu kasashen duniya da dama da za su rungumi amfani da kudin Sin RMB wajen huldar kasuwanci saboda kasancewar Sin a matsayin kasa mafi girman hada-hadar kasuwanci a duniya. Ko a kwanan baya, an ruwaito shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva yana kiran kasashen duniya su samar wa kansu mafita a kan amfani da dalar Amurka, domin a cewarsa me ya sa dukkan kasashen duniya ke amfani da dalar a kasuwancinsu.

Bugu da kari, gwamnatocin kasashen waje da ke bukatar adana kudaden ajiyarsu na waje da dalar Amurka za su kara kashe kudi wajen neman dalar, inda lamarin zai fi shafar tattalin arzikin kasashe masu tasowa saboda ribar da ake samu wajen fitar da kaya zuwa waje ta ragu.

Labarai Masu Nasaba

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Haka zalika, Rasha da Sin sun cimma yarjejeniya don fara biyan kudin iskar gas da take samarwa kasar Sin a kudin Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Har ila yau, masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin mai ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Yayin da wannan yunkuri na fita daga kangin dalar Amurka ke samun tagomashi, Kasashe masu kawancen bunkasa ci gabansu na BRICS (Brazil, Rasha, Indiya, Sin, da Afirka ta Kudu) suna shirin kaddamar da sabon kudin da kasashe mambobin kungiyar za su rika amfani da su wajen cinikayya a tsakaninsu. Haka nan gabanin taron kolin kungiyar BRICS na watan Agusta da za a yi a Afirka ta Kudu, yanzu haka akwai kasashe 24 da ke neman kulla kawance domin fita daga tarnakin da dalar Amurka ta yi musu na tsawon shekaru. Kasashen sun hada da Najeriya, Saudi Arabiya, Iran, Argentina, Hadaddiyar Daular Larabawa, Aljeriya, Masar, Bahrain, Indonesia da wasu kasashe na Afirka.

Ko a ’yan watannin baya, Kenya ta sauwake wa kanta nemo Dala Miliyan 500 duk wata don biyan kudin fetur da take shigo da shi, sakamakon kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings.

Ya kamata Nijeriya ta dauki darasi ta farfado da yarjejeniyar musanyar kudin nan a tsakaninta da Sin ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 da aka kulla a 2018, saboda kasuwancin dake tsakaninsu wanda ko a watanni ukun farko na shekarar nan ya kai kimanin Naira Tiriliyan Hudu da Biliyan Hamsin da Biyar da Miliyan Dari Biyu da Talatin da Takwas (4,055,238,000.00), kamar yadda aka ruwaito Jami’ar Ofishin Jakadancin Sin a Legas, Ms. Yan Yuqing tana fada a ’yan watannin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisar Dokokin NijeriyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Bude Bikin Baje Kolin Cinikayyar Hidima Na 2023 A Satumba

Next Post

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Related

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

40 minutes ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

2 hours ago
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

21 hours ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

22 hours ago
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
Daga Birnin Sin

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

23 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

24 hours ago
Next Post
Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.