• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Tabbatar Da Hakkin Dan Adam Cikin Rayuwar Jama’a

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata A Tabbatar Da Hakkin Dan Adam Cikin Rayuwar Jama’a

A woman sells food items at a market in Owo, Southwestern Nigeria, Tuesday, June 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya, mukaddashiyar babbar kwamishina mai kula da hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, Nada Al-Nashif ta bayyana a cikin wani jawabinta cewa, hauhawar farashin kayayyaki na haifar da barazana ga hakkin raya kai na jama’ar kasashe masu tasowa.

A cewarta, yayin da asusun ba da lamunin duniya IMF ke hasashen ganin matsakaiciyar hauhawar farashin kayayyaki ta kashi 6.6% a kasashe masu sukuni a shekarar da muke ciki, hauhawar da ake sa ran ganinta a kasashe masu tasowa za ta iya kaiwa kashi 9.5%, bisa wani matsakaicin matsayi.

  • Aikin Binciken Duniyar Mars Na Kasar Sin Ya Samu Kyawawan Sakamakon Kimiyya

Batun nan bai ba ni mamaki ba, ganin yadda tun tuni kasar Amurka ke sanya bankunan kasar ba da karin ruwan kudin ajiya, don neman daidaita matsalar hauhawar farashin kaya a cikin gidanta.

Sai dai matakin ya zama karkata matsin lamba da take fuskanta zuwa ga sauran kasashe, musamman ma kasashe marasa karfin tattalin arziki, wadanda suka fi jin radadin manufar.

A sakamakon haka, zuwa yanzu, darajar kudin Rand na kasar Afirka ta Kudu ta ragu da kashi 9.4%, yayin da darajar Pound na kasar Masar ta sauka da kashi 18%.

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

A kasar Ghana ma, ko da yake ta riga ta daga ruwan kudin ajiya zuwa kashi 22% don tinkarar matakin kasar Amurka, amma duk da haka, darajar kudin kasar na ci gaba da raguwa.

Kar mu manta da yadda kasar Amurka ke bayyana kanta a matsayin mai kare hakkin dan Adam a duniya. Amma ga shi yanzu tana kwatan moriya a kasashe marasa karfin tattalin arziki, tare da keta hakkin jama’ar kasashen na rayuwa da neman raya kansu.

Ta wannan misali za mu iya ganin cewa, “kare hakkin dan Adam” da kasar Amurka take yi aikin fatar baki ne kawai, wanda sam ba zai haifar da moriya ga mutanen duniya ba.

Sai dai a nata bangare, yadda kasar Sin take fahimtar matakin “mai dokar barci ya buge da gyangyadi” da kasar Amurka ke dauka a fannin kare hakkin dan Adam, ya sa kasar ke kira ga kasashe daban daban don su dora karin muhimmanci kan kare hakkin dan Adam na raya kai da neman ci gaba.

A gun taron kwamitin hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya dake gudana, wakilin Sin Chen Xu ya ce, ci gaban tattalin arziki shi ne tushen hakkin dan Adam. A cewarsa, ya kamata kasashe daban daban su yi kokarin tabbatar wa al’ummunsu hakki na gaske, kuma mai amfani.

Shin mene ne hakkin dan Adam na gaske kuma mai amfani?
Na tuna da wani saurayi mai aikin jigilar kaya da na gamu da shi a nan birnin Beijing a kwanan baya.

Ya ce, ko da yake aikin da yake yi na kai abincin da aka saya ta yanar gizo ta Internet zuwa gidajen mutanen da suka sayi abincin na da wahala, amma yana samun Yuan 7 (kwatankwacin dalar Amurka 1) bisa duk wani kunshi da ya kai.

Ya kan iya kai kunshi fiye da 100 a kowace rana, ta yadda yake samun fiye da Yuan 700 (fiye da dala 100) a duk rana.

Hakan zai tabbatar da albashinsa na kowane wata da ya kai fiye da Yuan 15000 (dala 2122). To, wadannan adadi su ne shaidar hakkin dan Adam na gaske.
Ban da wannan kuma na tuna da wani kauye mai suna “Xiao Hei Fa” da na kai ziyara a kwanan baya, inda na ga gwamnati na ba da tallafi ga wasu kamfanoni, domin su samar da guraben aikin yi ga mutane masu fama da lalurar nakasa.

Ta wannan hanya wadannan nakasassu sun samu kudin shigar da ya kai fiye da Yuan dubu 25 (dalar Amurka 3540) a duk shekara, abun da ya sa suke iya dokaro da kansu. Wannan irin manufar taimakawa nakasassu ita ce abin da ake kira manufar kare hakkin dan Adam mai amfani.

Hakkin dan Adam bai tsaya ga kalmomi kawai ba, ya kamata a yi kokarin tabbatar da shi a cikin rayuwar jama’a. Ta hanyar tantance yanayin rayuwar jama’a, za a san ainihin yanayin hakkin dan Adam na wata kasa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoman Kasar Sin Sun Gudanar Da Bikin Girbi Na Bana

Next Post

Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano – Kwamishina

Related

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

12 hours ago
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
Daga Birnin Sin

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

13 hours ago
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Daga Birnin Sin

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

14 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

15 hours ago
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
Daga Birnin Sin

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

16 hours ago
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
Daga Birnin Sin

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

18 hours ago
Next Post
Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano – Kwamishina

Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano - Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Jama’a Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.