• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Tabbatar Da Hakkin Dan Adam Cikin Rayuwar Jama’a

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata A Tabbatar Da Hakkin Dan Adam Cikin Rayuwar Jama’a

A woman sells food items at a market in Owo, Southwestern Nigeria, Tuesday, June 7, 2022. Nigeria's consumer inflation surged to a 17-year high in August 2022, its statistics agency said on Thursday, Sept. 15, 2022, signalling more hardship for citizens and businesses in Africa's largest economy. (AP Photo/Sunday Alamba)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya, mukaddashiyar babbar kwamishina mai kula da hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, Nada Al-Nashif ta bayyana a cikin wani jawabinta cewa, hauhawar farashin kayayyaki na haifar da barazana ga hakkin raya kai na jama’ar kasashe masu tasowa.

A cewarta, yayin da asusun ba da lamunin duniya IMF ke hasashen ganin matsakaiciyar hauhawar farashin kayayyaki ta kashi 6.6% a kasashe masu sukuni a shekarar da muke ciki, hauhawar da ake sa ran ganinta a kasashe masu tasowa za ta iya kaiwa kashi 9.5%, bisa wani matsakaicin matsayi.

  • Aikin Binciken Duniyar Mars Na Kasar Sin Ya Samu Kyawawan Sakamakon Kimiyya

Batun nan bai ba ni mamaki ba, ganin yadda tun tuni kasar Amurka ke sanya bankunan kasar ba da karin ruwan kudin ajiya, don neman daidaita matsalar hauhawar farashin kaya a cikin gidanta.

Sai dai matakin ya zama karkata matsin lamba da take fuskanta zuwa ga sauran kasashe, musamman ma kasashe marasa karfin tattalin arziki, wadanda suka fi jin radadin manufar.

A sakamakon haka, zuwa yanzu, darajar kudin Rand na kasar Afirka ta Kudu ta ragu da kashi 9.4%, yayin da darajar Pound na kasar Masar ta sauka da kashi 18%.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

A kasar Ghana ma, ko da yake ta riga ta daga ruwan kudin ajiya zuwa kashi 22% don tinkarar matakin kasar Amurka, amma duk da haka, darajar kudin kasar na ci gaba da raguwa.

Kar mu manta da yadda kasar Amurka ke bayyana kanta a matsayin mai kare hakkin dan Adam a duniya. Amma ga shi yanzu tana kwatan moriya a kasashe marasa karfin tattalin arziki, tare da keta hakkin jama’ar kasashen na rayuwa da neman raya kansu.

Ta wannan misali za mu iya ganin cewa, “kare hakkin dan Adam” da kasar Amurka take yi aikin fatar baki ne kawai, wanda sam ba zai haifar da moriya ga mutanen duniya ba.

Sai dai a nata bangare, yadda kasar Sin take fahimtar matakin “mai dokar barci ya buge da gyangyadi” da kasar Amurka ke dauka a fannin kare hakkin dan Adam, ya sa kasar ke kira ga kasashe daban daban don su dora karin muhimmanci kan kare hakkin dan Adam na raya kai da neman ci gaba.

A gun taron kwamitin hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya dake gudana, wakilin Sin Chen Xu ya ce, ci gaban tattalin arziki shi ne tushen hakkin dan Adam. A cewarsa, ya kamata kasashe daban daban su yi kokarin tabbatar wa al’ummunsu hakki na gaske, kuma mai amfani.

Shin mene ne hakkin dan Adam na gaske kuma mai amfani?
Na tuna da wani saurayi mai aikin jigilar kaya da na gamu da shi a nan birnin Beijing a kwanan baya.

Ya ce, ko da yake aikin da yake yi na kai abincin da aka saya ta yanar gizo ta Internet zuwa gidajen mutanen da suka sayi abincin na da wahala, amma yana samun Yuan 7 (kwatankwacin dalar Amurka 1) bisa duk wani kunshi da ya kai.

Ya kan iya kai kunshi fiye da 100 a kowace rana, ta yadda yake samun fiye da Yuan 700 (fiye da dala 100) a duk rana.

Hakan zai tabbatar da albashinsa na kowane wata da ya kai fiye da Yuan 15000 (dala 2122). To, wadannan adadi su ne shaidar hakkin dan Adam na gaske.
Ban da wannan kuma na tuna da wani kauye mai suna “Xiao Hei Fa” da na kai ziyara a kwanan baya, inda na ga gwamnati na ba da tallafi ga wasu kamfanoni, domin su samar da guraben aikin yi ga mutane masu fama da lalurar nakasa.

Ta wannan hanya wadannan nakasassu sun samu kudin shigar da ya kai fiye da Yuan dubu 25 (dalar Amurka 3540) a duk shekara, abun da ya sa suke iya dokaro da kansu. Wannan irin manufar taimakawa nakasassu ita ce abin da ake kira manufar kare hakkin dan Adam mai amfani.

Hakkin dan Adam bai tsaya ga kalmomi kawai ba, ya kamata a yi kokarin tabbatar da shi a cikin rayuwar jama’a. Ta hanyar tantance yanayin rayuwar jama’a, za a san ainihin yanayin hakkin dan Adam na wata kasa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manoman Kasar Sin Sun Gudanar Da Bikin Girbi Na Bana

Next Post

Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano – Kwamishina

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

15 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

16 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

17 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

18 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

19 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano – Kwamishina

Ana Bukatar Ruwa Lita Miliyan 200 A Kullum A Kano - Kwamishina

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.