• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya

by yahuzajere
4 months ago
in Kasashen Ketare
0
Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani abu da ya ja hankalina kuma ya jefa ni cikin tunani a kan abubuwan da ke faruwa a kan batun kare-karen harajin kwastam da Amurka ke yi a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta shi ne, yadda shahararren kamfanin nan na kera motoci na Amurka Tesla ya fara aiki kwanan nan a katafariyar masana’antar da ya gina a birnin Shanghai, babbar cibiyar hada-hadar kasuwanci ta kasar Sin.

Wannan ya nuna yadda kamafanin yake kara fadada harkokinsa na kasuwanci a kasar Sin. Kuma saboda yadda kamfanin ya samu saukin gudanar da harkokinsa albarkacin manufar kasar Sin ta kara bude kofarka ga kasashen waje, domin su shigo a dama da su a kasuwarta ta amfani da kayayyaki mafi girma a duniya, cikin watanni takwas kacal da fara aikin gidana sabuwar masana’antar, tuni har an fara sarrafa kayayyakin kamfanin gadan-gadan.

  • Babu Wata Tsokana Da Sojojin Amurka Za Su Yi Da Za Ta Iya Canza Matsayin Yankin Taiwan 
  • Amurka Ba Za Ta Cimma Burinta Bisa Matakin Kara Harajin Kwastam Kan Ma’adanan Karfe Da Goran Ruwa Ba

Masana’antar za ta fi mayar da hankali ce ga samar da manyan baturan makamashi da aka fi sani da “megapacks” inda za ta rika kera rukunan batura a kalla 10,000 masu makamashin da ya kai karfin sa’o’in gigawatt 40, a duk shekara a farkon fara aiki.

Fadin kadadar filin kamfanin ya kai murabba’in mita 200,000, kana jarin da aka zuba a sabuwar masana’antar ya kai dala miliyan 202 wanda tabbas manuniya ce ga irin amincin da kamfanonin Amurka suka samu a kasar Sin na gudanar da harkokinsu ba tare da fargaba ba.

Kazalika, ba kamfanin Tesla ne kawai yake cin moriyar kasar Sin ba, akwai wasu kamfanonin Amurka da dama dake ci gaba da samun bunkasa a kasar. Ga misali, kamfanoni irin su General Motors, Ford, da Boeing duk suna da hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin, da ke kera motoci da na’urorin jiragen sama a biranen Shanghai da Chengdu.

Labarai Masu Nasaba

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Har ila yau, ga irin su Apple, Microsoft, da Google da duk sun samu gindin zama a kasar Sin tare da bude ofisoshi da ressan masana’antu a biranen Shanghai, Beijing, da Shenzhen.

Haka nan sauran kamfanoni irin su Coca-Cola, da PepsiCo duk sun tsayu da kafafunsu sosai a kasar. Bugu da kari, ga kamfanonin harkokin biyan kudi ta fasahar zamani kamarsu Amazon da PayPal da su ma suka samu hadin kan kamfanonin kasar Sin don fadada kasuwancinsu a cikin kasar.

Duka wannan yana nuna yadda Sin ke fada da cikawa ne a kan manufofinta na kara bude kofa ga duniya. Kuma ya dace Amurka ta nuna sanin ya kamata a kan bahaguwar fahimtarta da sake lale kan matakanta na haddasa fitina a bangaren kasuwancin duniya.

Sannan ko da za ta nace a kan tana da ikon kara haraji a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta, to ta sani, ita ma tana da kamfanoni a kasashen waje da aka yi masu riga da wando, kuma masu karin magana sun ce, “ana barin halal don kunya!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKunya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴan Bindiga Sun Buɗe Sabuwar Daba A Jihar Zamfara

Next Post

Ba Wani Maniyyacin Da Zai Rasa Aikin Hajjin 2025 – Mataimakin Shugaban kasa

Related

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

1 day ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

3 days ago
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
Kasashen Ketare

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

4 days ago
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Kasashen Ketare

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

6 days ago
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

1 week ago
Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
Kasashen Ketare

Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9

2 weeks ago
Next Post
Ba Wani Maniyyacin Da Zai Rasa Aikin Hajjin 2025 – Mataimakin Shugaban kasa

Ba Wani Maniyyacin Da Zai Rasa Aikin Hajjin 2025 – Mataimakin Shugaban kasa

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

Bilicin: NAFDAC Ta Kama Mutane 6, Ta Rufe Shaguna A Kano

June 25, 2025
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.