ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya

by yahuzajere
1 year ago
amurka

Wani abu da ya ja hankalina kuma ya jefa ni cikin tunani a kan abubuwan da ke faruwa a kan batun kare-karen harajin kwastam da Amurka ke yi a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta shi ne, yadda shahararren kamfanin nan na kera motoci na Amurka Tesla ya fara aiki kwanan nan a katafariyar masana’antar da ya gina a birnin Shanghai, babbar cibiyar hada-hadar kasuwanci ta kasar Sin.

Wannan ya nuna yadda kamafanin yake kara fadada harkokinsa na kasuwanci a kasar Sin. Kuma saboda yadda kamfanin ya samu saukin gudanar da harkokinsa albarkacin manufar kasar Sin ta kara bude kofarka ga kasashen waje, domin su shigo a dama da su a kasuwarta ta amfani da kayayyaki mafi girma a duniya, cikin watanni takwas kacal da fara aikin gidana sabuwar masana’antar, tuni har an fara sarrafa kayayyakin kamfanin gadan-gadan.

  • Babu Wata Tsokana Da Sojojin Amurka Za Su Yi Da Za Ta Iya Canza Matsayin Yankin Taiwan 
  • Amurka Ba Za Ta Cimma Burinta Bisa Matakin Kara Harajin Kwastam Kan Ma’adanan Karfe Da Goran Ruwa Ba

Masana’antar za ta fi mayar da hankali ce ga samar da manyan baturan makamashi da aka fi sani da “megapacks” inda za ta rika kera rukunan batura a kalla 10,000 masu makamashin da ya kai karfin sa’o’in gigawatt 40, a duk shekara a farkon fara aiki.

ADVERTISEMENT

Fadin kadadar filin kamfanin ya kai murabba’in mita 200,000, kana jarin da aka zuba a sabuwar masana’antar ya kai dala miliyan 202 wanda tabbas manuniya ce ga irin amincin da kamfanonin Amurka suka samu a kasar Sin na gudanar da harkokinsu ba tare da fargaba ba.

Kazalika, ba kamfanin Tesla ne kawai yake cin moriyar kasar Sin ba, akwai wasu kamfanonin Amurka da dama dake ci gaba da samun bunkasa a kasar. Ga misali, kamfanoni irin su General Motors, Ford, da Boeing duk suna da hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin, da ke kera motoci da na’urorin jiragen sama a biranen Shanghai da Chengdu.

LABARAI MASU NASABA

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Har ila yau, ga irin su Apple, Microsoft, da Google da duk sun samu gindin zama a kasar Sin tare da bude ofisoshi da ressan masana’antu a biranen Shanghai, Beijing, da Shenzhen.

Haka nan sauran kamfanoni irin su Coca-Cola, da PepsiCo duk sun tsayu da kafafunsu sosai a kasar. Bugu da kari, ga kamfanonin harkokin biyan kudi ta fasahar zamani kamarsu Amazon da PayPal da su ma suka samu hadin kan kamfanonin kasar Sin don fadada kasuwancinsu a cikin kasar.

Duka wannan yana nuna yadda Sin ke fada da cikawa ne a kan manufofinta na kara bude kofa ga duniya. Kuma ya dace Amurka ta nuna sanin ya kamata a kan bahaguwar fahimtarta da sake lale kan matakanta na haddasa fitina a bangaren kasuwancin duniya.

Sannan ko da za ta nace a kan tana da ikon kara haraji a kan kayayyakin da ake shigo da su kasarta, to ta sani, ita ma tana da kamfanoni a kasashen waje da aka yi masu riga da wando, kuma masu karin magana sun ce, “ana barin halal don kunya!” (Abdulrazaq Yahuza Jere)

amurka
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin
  • yahuzajere
    Wani Asibiti A Kano Ya Ƙaddamar Da Na’urar Kula Da Jarirai Irinta Ta Farko A Arewacin Nijeriya

MASU ALAKA

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei
Kasashen Ketare

Iran Za Ta Rufe Tehran A Mako Mai Zuwa Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

July 1, 2026
Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Next Post
Ba Wani Maniyyacin Da Zai Rasa Aikin Hajjin 2025 – Mataimakin Shugaban kasa

Ba Wani Maniyyacin Da Zai Rasa Aikin Hajjin 2025 – Mataimakin Shugaban kasa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.