• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar kalaman wasu ’yan siyasar Amurka, ba zai rasa jin kalamai dake bayyana kasar Sin a matsayin abokiyar hamayya ko taraka da ya wajaba Amurka ta takawa birki ba.

A daya hannun kuwa, kasar Sin ta sha bayyana wannan mahanga ta Amurka a matsayin kuskure, tare da nanata kira ga Amurka da ta rika kallon alakar dake tsakanin kasashen biyu sama da batun takara kadai, domin kuwa a matsayinsu na manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya, Sin da Amurka na iya gudanar da hadin gwiwa da cudanya mai tsafta, ba tare da shiga takun saka ko fito na fito ba.

  • Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

Karkashin matakan da Amurka ke dauka, na bayyana adawa a zahiri ga Sin, an ga yadda take yin matsin lamba ga halastattun hakkokin wasu kamfanonin Sin, tare da kakkaba musu takunkumai, inda a wasu lokutan hakan kan kawo tsaiko ga tsarin samar da hajojin masana’antu na duniya.

Ko da yake shugabannin Amurka a wasu lokacin kan ce ba su da nufin haifar da tashin hankali tsakaninsu da bangaren Sin, amma matakai na zahiri da suke dauka na sabawa hakan, musamman duba da cewa, har kullum Amurka tana jaddada aniyar nan ta “Sanya bukatu da muradun kasar gaban komai”, ba tare da la’akari da bukatar wanzar da daidaito da lura da bukatun sauran sassan duniya ba.

Ko shakka babu duniya na da fadin da kasashen biyu za su iya aiwatar da dukkanin matakan raya kansu yadda ya kamata, ba tare da sun hari juna, ko sun shiga cacar baka maras amfani ba. Kazalika wanzar da kyakkyawar alaka tsakanin Sin da Amurka, zai kare moriyar al’ummunsu baki daya, tare da burikan da sauran sassan kasa da kasa suke fatan ganin an cimma.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Yayin da kasar Sin ke ta kokarin ganin ta inganta alakarta da Amurka, karkashin manufofin martaba juna, da kaucewa mummunar takara, da zama da juna lami lafiya, da gudanar da hadin gwiwa don cimma moriya tare, ya kamata a nata bangare ita ma Amurka ta yi watsi da ra’ayin nan na “Ko na samu ko kowa ya rasa”.

Bugu da kari, dukkanin wata nasara da kasashen 2 za su samu, za su kasance damammaki na bunkasar dukkanin sassan duniya, don haka ya zama wajibi Amurka ta sauya mahangarta game da Sin, ta kalli Sin a matsayin abokiyar cudanya da za a yi tarayya da ita wajen wanzar da ci gaba mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Takunkumin Da Amurka Ke Sanyawa Kasar Sham Na Tsananta Matsalar Jin Kai Da Kasar Ke Fuskanta

Next Post

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Related

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

41 minutes ago
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

21 hours ago
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

22 hours ago
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

23 hours ago
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu
Daga Birnin Sin

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

24 hours ago
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani
Daga Birnin Sin

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

1 day ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

July 28, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

July 28, 2025
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

July 28, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe

July 28, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin Bai Wa Malaman Manyan Makarantun Nijeriya Rancen Miliyan 10

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.