• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar kalaman wasu ’yan siyasar Amurka, ba zai rasa jin kalamai dake bayyana kasar Sin a matsayin abokiyar hamayya ko taraka da ya wajaba Amurka ta takawa birki ba.

A daya hannun kuwa, kasar Sin ta sha bayyana wannan mahanga ta Amurka a matsayin kuskure, tare da nanata kira ga Amurka da ta rika kallon alakar dake tsakanin kasashen biyu sama da batun takara kadai, domin kuwa a matsayinsu na manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya, Sin da Amurka na iya gudanar da hadin gwiwa da cudanya mai tsafta, ba tare da shiga takun saka ko fito na fito ba.

  • Kasar Sin Na Samar Da Agajin Jin Kai Ga Wadanda Girgizar Kasa Ta Shafa A Syria

Karkashin matakan da Amurka ke dauka, na bayyana adawa a zahiri ga Sin, an ga yadda take yin matsin lamba ga halastattun hakkokin wasu kamfanonin Sin, tare da kakkaba musu takunkumai, inda a wasu lokutan hakan kan kawo tsaiko ga tsarin samar da hajojin masana’antu na duniya.

Ko da yake shugabannin Amurka a wasu lokacin kan ce ba su da nufin haifar da tashin hankali tsakaninsu da bangaren Sin, amma matakai na zahiri da suke dauka na sabawa hakan, musamman duba da cewa, har kullum Amurka tana jaddada aniyar nan ta “Sanya bukatu da muradun kasar gaban komai”, ba tare da la’akari da bukatar wanzar da daidaito da lura da bukatun sauran sassan duniya ba.

Ko shakka babu duniya na da fadin da kasashen biyu za su iya aiwatar da dukkanin matakan raya kansu yadda ya kamata, ba tare da sun hari juna, ko sun shiga cacar baka maras amfani ba. Kazalika wanzar da kyakkyawar alaka tsakanin Sin da Amurka, zai kare moriyar al’ummunsu baki daya, tare da burikan da sauran sassan kasa da kasa suke fatan ganin an cimma.

Labarai Masu Nasaba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Yayin da kasar Sin ke ta kokarin ganin ta inganta alakarta da Amurka, karkashin manufofin martaba juna, da kaucewa mummunar takara, da zama da juna lami lafiya, da gudanar da hadin gwiwa don cimma moriya tare, ya kamata a nata bangare ita ma Amurka ta yi watsi da ra’ayin nan na “Ko na samu ko kowa ya rasa”.

Bugu da kari, dukkanin wata nasara da kasashen 2 za su samu, za su kasance damammaki na bunkasar dukkanin sassan duniya, don haka ya zama wajibi Amurka ta sauya mahangarta game da Sin, ta kalli Sin a matsayin abokiyar cudanya da za a yi tarayya da ita wajen wanzar da ci gaba mai ma’ana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Takunkumin Da Amurka Ke Sanyawa Kasar Sham Na Tsananta Matsalar Jin Kai Da Kasar Ke Fuskanta

Next Post

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Related

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
Daga Birnin Sin

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

18 hours ago
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

18 hours ago
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

19 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

20 hours ago
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

21 hours ago
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

22 hours ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.