• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

by Khalid Idris Doya
4 months ago
in Siyasa
0
Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar ZLP a Jihar Bauchi, ta bukaci babban lauya, Eko Ejembi (SAN) da abokan aikinsa da su fara shirye-shiryen daukar matakan shari’a kan kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP bisa bayyana cewa dan takarar jam’iyyar a Jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa ya koma PDP tare da janye takararsa.

Idan ba a manta ba a ranar Talata kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya ziyarci Jihar Bauchi domin yakin zabensa, inda kusoshi na jam’iyyar ciki har da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar da gwamna Bala Muhammad suka halarta, inda aka bayyana sunayen wasu da suka koma PDP ciki har da ayyana sunan dan takarar gwamna na jam’iyyar ZLP.

  • Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
  • Na Yi Alkawari Zan Kawar Da Matsalolin Al’umma, In Ji Tinubu

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a ranar Alhamis, dan takarar, ya karyata labarin, ya kuma nuna bacin ransa tare da cewa kwata-kwata babu wanda ya tuntubesa kan wannan zance.

“Ina zaune a ofis ina ganawa da wasu sai aka fara kirana a waya ana tambayata, ya aka yi aka ji sunana cewa na koma PDP?

“Na ce ban gane ba, wace magana ce wannan?. Wasa gaske na amsa kiran waya kan wannan batun a lokacin sama da 100, inda magoya bayanmu suna nuna takaicinsu da nuna bacin ransu da jin wannan maganar.

Labarai Masu Nasaba

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

“Gaskiya ni ban san da wannan batu ba kuma ba a yi wannan zancen da ni ba. Kuma ba mu shirya cewa zan sauya sheka na koma wata jam’iyya ba.

“Kowa ya ga yadda muka karbu a Jihar Bauchi, babu wani matashi kamata a duk ‘yan takarar nan, ni ne mai karancin shekaru kuma matasa suna alfahari da hakan. Sun kuma shirya wajen ganin nasu ya karbi mulki. Alhamdullahi muna kallon nasara domin tsakaninmu idan har aka yi zabe bisa gaskiya to ni zan ci, sai dai idan magudi za a yi.”

Ya ce, ya fito ya barranta kansa da wannan ikirarin da PDP da ‘yan takaranta suka yi a gaban dubban jama’a.

“Na rubuta wasika zuwa ga babban lauya na kasa kuma muna jiran amsarsa, domin ka san mai neman shugaban kasa zan yi kara Atiku Abubakar da Dino Melaye da ya kira sunana, da kuma shugaban jam’iyyar PDP na kasa Iyorchia Ayu, da shugaban PDP na Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam.”

Arewa, ya sha alwashin samun nasara a zaben gwamna na 11 ga watan Maris, 2023.

“Wannan bata suna ne baro-baro a matsayina na dan takarar gwamna da nake kallon zan ci zabe, yanzu a sakamakon wannan furucin da suka yi na rasa akalla kashi 30 na magoya bayana.

“Wani daga jin wannan batun shi ke nan ya tafi da shi a ransa ke nan, wani kuma zai ga tun farko yaudararsa aka yi, wani kuma zai ga ban kyauta wa masoyana ba, kowa da yadda zai dauki batun, don haka ba lamari ne da za mu bar shi haka nan ba.”

Arewa ya ce, kwata-kwata babu wata yarjejeniya da suka yi da gwamnatin Jihar Bauchi ko PDP kan cewa zai janye takararsa ba.

“Idan ma za mu janye ya kamata a ji nunfashinmu balle ma hakan baya daga cikin manufarmu. Shin an ma fito an fadi hakan a kan mu don an fi mu cancanta ne ko don rainin da aka mana? Ko kuma a’a fahimtarmu ce ta zo daya, amma babu haka kawai mutum ya tashi kawai ya ce mun janye neman takararmu hakan ba za ta yiwuwa ba.”

A kwafin wasikar da ZLP ta aike wa Lauyoyin ta ce, “Daukan matakin shari’ar shi ne zai dawo wa jam’iyyarmu da kima da mutuncinta kan yarfen da aka mana.”

Wasikar mai dauke da sanya hannun Ambasada Khalid Arewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar, “Kwasam a ranar 7 ga watan Fabrairu, 2023 PDP-PCC ya kira sunan dan takarar gwamnanmu a jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa da cewa ya koma jam’iyyar PDP, wannan furucin ya janyo mana asara sosai da jawo damuwa.”

“Tun lokacin da PDP ta fito ta yi wannan furucin, magoya baya da masoyan ZLP sun shiga damuwa sun kuma nuna rashin jin dadinsu a sassa daban-daban na kananan hukumomin jihar Bauchi.”

Tags: ArewaBauchiSiyasaZLP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin

Next Post

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Related

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara
Siyasa

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

23 hours ago
Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim
Siyasa

Duk Ɗan Siyasar Da Ya Shiga Rigar Kwankwaso Ya Kauce Hanya Zai Gani A 2027 – Alhaji Ibrahim

1 day ago
Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe
Siyasa

Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe

2 days ago
Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima
Siyasa

Kwana 2 Kafin Rantsuwa: Kotun Koli Ta Yi Watsi Da Karar PDP Kan Takarar Tinubu Da Shettima

1 week ago
Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia
Siyasa

Jam’iyyar Labour Ta Yi Fatali Da Hukuncin Da Kotu Ta Yanke Kan Zababben Gwamnan Abia

2 weeks ago
Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
Manyan Labarai

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

LABARAI MASU NASABA

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

June 4, 2023
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

June 3, 2023
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Tsarin Wayewar Kan Kasar Sin Mai Dacewa Da Zamani

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Tsarin Wayewar Kan Kasar Sin Mai Dacewa Da Zamani

June 3, 2023
Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Wuraren Al’adun Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Ziyarar Shugaba Xi Jinping A Wuraren Al’adun Sin Tana Da Babbar Ma’ana

June 3, 2023
Sin Ta Jaddada Kira Ga Sassan Masu Ruwa Da Tsaki A Rikicin Sudan Da Su Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta

Sin Ta Jaddada Kira Ga Sassan Masu Ruwa Da Tsaki A Rikicin Sudan Da Su Gaggauta Dakatar Da Bude Wuta

June 3, 2023
Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

Rashin Lafiyar Maigidana Ne Babban Tashin Hankalin Da Na Fuskanta A Vila – Aisha Buhari

June 3, 2023
‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa Ayarin Yahaya Bello Hari, Sun Raunata Jami’an Tsaro

June 3, 2023
Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Shugaban Eritrea Da Takwaransa Na Congo Kinshasa Sun Yabawa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

June 3, 2023
Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?

Wane Ne Sabon Kocin Chelsea Mauricio Po-chettino?

June 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.