• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Atiku Ya Nemi Afuwar ‘Yan Nijeriya – Sanata Adeyemi

by Sadiq
3 years ago
Adeyemi

Sanata Smart Adeyemi, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya roki gafarar ‘yan Nijeriya maimakon neman kujerar shugaban kasa.

Adeyemi, wanda ke wakiltar Kogi ta Yamma a Majalisar Dokoki, ya bayyana haka ne a lokacin da yake tattaunawa da ’yan asalin Jihar Kogi mazauna Minna a ranar Talata a wani taron mara wa Tinubu da Shettima baya.

  • Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 
  • Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Ya ce ya kamata tsohon mataimakin shugaban kasar ya nemi afuwar ‘yan Nijeriya kan sayar da dukiyar kasa baki daya.

“Atiku karkashin kulawarsa a matsayinsa na shugaban kamfanonin kasuwanci, ya sayar da dukiyoyinmu na gama-gari, kuma shi ne tushen talauci da rashin tsaro a Nijeriya.

“Don haka Atiku ya kamata ya fara bai wa ‘yan Nijeriya hakuri kan yadda suka kashe Naira biliyan 16 don samar da wutar lantarki amma ba mu da wutar lantarki ta sa’o’i 24.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

“Ya kamata Atiku ya bayyana mana irin yadda suka karkatar da dukiyar gwamnati wanda ko shakka babu ya hada da rashin tsaro da tattalin arzikin Nijeriya a yau sakamakon aika-aikar da PDP ta yi wanda Atiku Abubakar ya jagoranta,” in ji shi.

Sai dai Sanatan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su marawa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da Kashim Shettima baya ya kara da cewa dukkansu mutane ne masu gaskiya.

“Abin da Nijeriya ke bukata a yanzu shi ne mutum mai hangen nesa ta yadda za a inganta rayuwarmu, ta yadda za mu ci moriyar tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma tattalin arzikin kasar nan ya kai wani matsayi mai girma,” in ji shi.

Ya bayyana Tinubu da Shettima a matsayin wani babban hadin kai.

A nasa jawabin, Gwamna Abubakar Sani-Bello na Jihar Neja, ya yi tir da halin da kasar nan ke ciki idan ya kwatanta shi da yadda ta kasance kafin shekarar 1999, ya kuma shawarci ‘yan Nijeriya da su zabi shugabannin da suka cancanta da za su fitar da kasar nan daga halin da ta ke ciki.

“Halin da Nijeriya ke ciki kafin 1999 da abin da yake faruwa a yanzu ya sa na koka kan makomar ‘ya’yanmu.

“Amma yanayin da muke ciki a yau abun bakin ciki ne kuma abin da Nijeriya ta kasance a yau yana da matukar tausayi,” in ji shi.

Bello ya yaba wa al’ummar Kogi mazauna jihar tare da yin kira a gare su da sauran wadanda ba ‘yan asalin jihar ba da su mara wa jam’iyyar APC baya su zabi duk ‘yan takararta.

A nasa jawabin, Sarkin Ebira a Neja, Alhaji Mansu Abdul, ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC a matakin jiha da kasa baki daya.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya rawaito cewa taron ya kuma shaida rabon kayan aiki ga mutanen Kogi mazauna Neja.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
Manyan Labarai

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

'Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Wata Tankar Mai Ta Sake Fashewa A Neja

Da Ɗumi-ɗumi: Fashewar Tankar Man Fetur Ta Yi Ajalin Rayuka 30 A Neja

October 21, 2025
Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

Sin Ta Bayar Da Tallafin Dala Miliyan 3.5 Ga Shirin Samar Da Abinci A Zambia

October 21, 2025
Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.