• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Atiku Ya Nemi Afuwar ‘Yan Nijeriya – Sanata Adeyemi

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Ya Kamata Atiku Ya Nemi Afuwar ‘Yan Nijeriya – Sanata Adeyemi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Smart Adeyemi, ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya roki gafarar ‘yan Nijeriya maimakon neman kujerar shugaban kasa.

Adeyemi, wanda ke wakiltar Kogi ta Yamma a Majalisar Dokoki, ya bayyana haka ne a lokacin da yake tattaunawa da ’yan asalin Jihar Kogi mazauna Minna a ranar Talata a wani taron mara wa Tinubu da Shettima baya.

  • Cikin Shekaru 3 Da Suka Gabata Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Yaki Da Annobar COVID-19 
  • Emefiele Ya Bayyana A Gaban Majalisa Kan Sauya Fasalin Kudi

Ya ce ya kamata tsohon mataimakin shugaban kasar ya nemi afuwar ‘yan Nijeriya kan sayar da dukiyar kasa baki daya.

“Atiku karkashin kulawarsa a matsayinsa na shugaban kamfanonin kasuwanci, ya sayar da dukiyoyinmu na gama-gari, kuma shi ne tushen talauci da rashin tsaro a Nijeriya.

“Don haka Atiku ya kamata ya fara bai wa ‘yan Nijeriya hakuri kan yadda suka kashe Naira biliyan 16 don samar da wutar lantarki amma ba mu da wutar lantarki ta sa’o’i 24.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

“Ya kamata Atiku ya bayyana mana irin yadda suka karkatar da dukiyar gwamnati wanda ko shakka babu ya hada da rashin tsaro da tattalin arzikin Nijeriya a yau sakamakon aika-aikar da PDP ta yi wanda Atiku Abubakar ya jagoranta,” in ji shi.

Sai dai Sanatan ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su marawa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu da Kashim Shettima baya ya kara da cewa dukkansu mutane ne masu gaskiya.

“Abin da Nijeriya ke bukata a yanzu shi ne mutum mai hangen nesa ta yadda za a inganta rayuwarmu, ta yadda za mu ci moriyar tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma tattalin arzikin kasar nan ya kai wani matsayi mai girma,” in ji shi.

Ya bayyana Tinubu da Shettima a matsayin wani babban hadin kai.

A nasa jawabin, Gwamna Abubakar Sani-Bello na Jihar Neja, ya yi tir da halin da kasar nan ke ciki idan ya kwatanta shi da yadda ta kasance kafin shekarar 1999, ya kuma shawarci ‘yan Nijeriya da su zabi shugabannin da suka cancanta da za su fitar da kasar nan daga halin da ta ke ciki.

“Halin da Nijeriya ke ciki kafin 1999 da abin da yake faruwa a yanzu ya sa na koka kan makomar ‘ya’yanmu.

“Amma yanayin da muke ciki a yau abun bakin ciki ne kuma abin da Nijeriya ta kasance a yau yana da matukar tausayi,” in ji shi.

Bello ya yaba wa al’ummar Kogi mazauna jihar tare da yin kira a gare su da sauran wadanda ba ‘yan asalin jihar ba da su mara wa jam’iyyar APC baya su zabi duk ‘yan takararta.

A nasa jawabin, Sarkin Ebira a Neja, Alhaji Mansu Abdul, ya yi alkawarin bayar da cikakken goyon baya ga dukkan ‘yan takarar jam’iyyar APC a matakin jiha da kasa baki daya.

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), ya rawaito cewa taron ya kuma shaida rabon kayan aiki ga mutanen Kogi mazauna Neja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abubakar Sani BelloAtikuKogiNejaPDPSanata Adeyemitakara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Ci Gaba Da Tattaunawa Da Kwankwaso Da Obi Kan Mara Min Baya – Atiku 

Next Post

‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

11 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

18 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

21 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

22 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

'Yansanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Sace Kananan Yara 2 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.