• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Kamata Kasashen Yamma Su Yi Hangen Nesa Game Da Tasirin Rikicin Ukraine Kan Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tuni farashin kayayyakin amfanin gona ya yi tashin gwauron zabi a sassan duniya daban daban, sakamakon rikicin Rasha da Ukraine, wanda a yanzu ya zarce watanni uku da barkewa.

Alkaluman shirin samar da abinci na MDD sun tabbatar da cewa, duniya ba ta taba ganin kalubalen tsadar cimaka sama da na wannan lokaci ba, tun bayan yakin duniya na biyu, lamarin da kuma ke zuwa a gabar da duniya ke fuskantar tasirin annobar COVID-19, wadda ita ma ta haifar da komadar tattalin arzikin duniya.

  • Jawabin Xi Jinping Ya Kara Azama Kan Aiwatar Da Shawarar Bunkasa Duniya

Yayin da kasashen yammacin duniya ke ta kokarin dora alhakin hauhawar farashin kayayyakin amfanin gona ga kasar Rasha, su ma a nasu bangare sun taka rawar gani wajen ingiza girman wannan matsala.

Ga misali, shi kan shi rikicin Rasha da Ukraine, kasashe biyu masu fitar da tarin albarkatun gona ga sassa daban daban na duniya, ya samo asali ne sakamakon kokarin fadada ikon kungiyar tsaro ta NATO zuwa gabashin turai. Kuma duk da yunkuri da aka yi na hawa teburin shawara tsakanin Rasha da Ukraine, Amurka a nata bangare, ta yi ta kokarin rura wutar rikicin ta hanyar samarwa Ukraine makamai domin tunkarar Rasha, wanda hakan ke kara tsawaita mummunan tasirin tashin hankalin.

A zahiri, tsawaitar wannan tashin hankali zai ci gaba da ingiza asarar da Rasha da Ukraine za su kirga, a hannu guda kuma, hakan zai haifar da kamfar abinci a sassa masu yawa na duniya, musamman kasashe masu tasowa, dake dogaro sosai kan cimakar da ake fitarwa daga kasashen biyu.

Labarai Masu Nasaba

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Ko shakka ba bu, yunkurin Amurka na kakaba takunkumin cinikayyar albarkatun gona da takin zamani da kasar Rasha ke fitarwa, ya haifar da hauhawar farashin cimaka da kaso sama da 30 bisa dari a kasashe masu tasowa.

Irin wadannan kasashe masu tasowa, da sauran masu raunin tattalin arziki, na shan matsin lambar rayuwa, sakamakon manufofin takara, da kokarin tabbatar da iko na wasu kasashen yamma, wannan yanayi ne da bai dace ba, domin kuwa, kamata yayi manyan kasashen yamma masu karfin fada a ji, su taimaka wajen fitar da kasashe masu tasowa daga wahalhalu, maimakon aiwatar da matakai na kara jefa su cikin mawuyacin hali. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Batun Mika ‘Yan Gudun Hijira Ya Nuna Halayyar Kasashen Yamma

Next Post

Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

Related

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

39 minutes ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

2 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

3 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

4 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

5 hours ago
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
Daga Birnin Sin

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

1 day ago
Next Post
Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

Yadda Wata Budurwa Ta Yi Garkuwa Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.