• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Makomar mai koyarwa Erik ten Hag a Manchester United ita ce abar da ake tattaunawa musamman ga masu sharhi a kan kwallon kafa da kuma magoya bayan kungiyar ta kasar Ingila.

Sai dai har yanzu akwai wadanda suke ganin akwai bukatar a sake ba wa dan kasar Holland din dama zuwa kakar wasa ta gaba domin a ganinsu zai iya dawo da kungiyar hayyacinta.

  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba
  • Gwamnan Zamfara Ya Sauke Nauyin Bashin Haƙƙoƙin Ma’aikata Na Fiye Da Naira Biliyan 4

Manchester United ta kasa samun gurbin komawa cikin masu fatan buga gasar Zakarun Turai a badi, bayan da Crystal Palace ta yi raga-raga da ita da ci 4-0 ranar Litinin a filin wasa na Selhurst Park.

Kungiyoyin sun kara a gasar mako na 36 a babbar gasar firimiya ta Ingila da suka fafata a Selhurst Park kuma Crystal Palace ta fara cin kwallo ta hannun Michael Olise daga baya Jean-Philippe Mateta ya kara ta biyu saura minti biyar su je hutun rabin lokaci.

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne Crystal Palace ta kara zura kwallaye biyu a ragar United ta hannun Tyrick Mitchell da kuma Michael Olise, wanda ya ci ta biyu a karawar. Wannan shi ne wasa na uku da suka fuskanci juna, bayan da Manchester United ta fara cin 3-0 a League Cup cikin Satumba kuma kwana hudu tsakani Palace ta shiga Old Trafford ta doke United 1-0, inda Joachim Andersen ne ya ci kwallon a minti na 25.

Wannan shi ne karo na biyu da Palace ta zura kwallaye da yawa a ragar Manchester United tun bayan 5-0 ranar Asabar 16 ga watan Disambar 1972 tun a gasar rukunin farko. Kawo yanzu a wannan kakar an zura kwallo 81 a ragar Manchester United a dukkan fafatawa a bana, kakar da kwallaye da yawa suka shiga ragarta tun 81 da aka dura mata a 1976 zuwa 1977.

Da wannan sakamakon Manchester United tana ta takwas a teburin Premier League da maki 54, iri daya da na Chelsea ta bakwai, wadda ta ci West Ham 5-0 ranar Lahadi, sai

Crystal Palace ta hada maki uku kenan ya zama 43 tana nan a matakinta na 14 a kasan teburin Premier da tazarar maki daya tsakaninta da Fulham ta 13. Sauran wasa biyu ya rage a gaban Crystal Palace da za ta je Wolberhampton a karshen mako, sannan ta karbi bakuncin Aston Billa a wasan karshe yayin da United kuwa wasa uku ne a gabanta, wadda za ta karbi bakuncin Arsenal da kuma Newcastle, sannan ta karkare da zuwa gidan Brighton.

United tana fatan daukar kofi a bana shi ne FA Cup da za ta fafata da Manchester City a wasan karshe.

Ina Matsalar Take?

Manchester United ta saka dukkan ‘yan wasanta a kasuwa, bayan da take fatan hada kudin da za ta bunkasa kungiyar karkashin INEOS daga badi kuma United ta kashe Yuro biliyan 1 a shekaru da yawa wajen sayen ‘yan wasan dake buga mata wasa, amma ta kasa taka rawar gani a kaka da yawa har da karkashin mai koyarwa Erik ten Hag.

Wannan ce kaka ta biyu da Ten Hag ya ja ragamar United, wanda ya dauki Carabao Cup a bara da samun gurbin Champions League a bara amma sai dai a bana an yi waje da kungiyar daga gasar Zaratun Turai cikin rukuni, sannan aka fitar da ita a Carabao Cup, bayan rashin nasara a hannun Newcastle United.

 Sannan da yake kungiyar ba za ta samu gurbin shiga Champions League a badi ba, ya zama wajibi ta rabu da wasu ‘yan kwallon a bana, domin ta samu gudanar da kungiyar kan cin riba.

Albashin da Manchester United kan biya ‘yan wasanta ya Fam miliyan £331, kuma matsakaicin dan wasa da ake biya duk mako shi ne Fam 54,000, sannan United ce ta hudu a biyan albashi mai tsoka tsakanin kungiyoyin Premier League, idan ka cire Manchester City da Chelsea da kuma Liberpool.

Manchester United tana ta takwas a teburin Premier League da maki 54, bayan cin wasa 16 aka doke ta 13 da canajaras shida sannan kungiyar ta ci kwallo 52 a Premier League a kakar nan, aka zura mata 55 a raga a babbar gasar firimiya ta Ingila.

Zuwa Kofin Zakarun turai

Yanzu dama biyu ta rage wa Manchester United, domin samun gurbin shiga gasar cin kofin Zakarun Turai ta 2024 zuwa 2025 amma duk da haka ba za ta buga kofin Zakarun Turai ba.

Gasar farko kenan da watakila da rarar kwallaye za a bi ta a raga, wadda ta taba yin haka a 1989 zuwa 1990, lokacin ta kare kakar a mataki na 13 a teburi kuma watakila kafin karshen wannan kakar ma kungiyar za ta iya yin kasa da haka.

Wannan shi ne karon farko da aka ci Manchester United wasa 13 a kaka daya a babbar gasar firimiya ta Ingila sai dai kociyan da suka ja ragamarta a kakar da ta yi rashin nasara 12 a 2013 zuwa 2014 da kuma kakar 2021 zuwa 2022.

To amma ta taba rashin nasara 16 a gasar rukunin farko a 1989 zuwa 1990, wadda ta karkare a mataki na 13 a teburin gasar amma a wannan kakar Manchester United an zura mata kwallaye 81 a dukkan karawar da take yi a bana, wadda aka taba durawa 81 a kakar wasa ta 1976 zuwa 1977.

Sauran wasa uku ya rage a gaban Manchester United, wadda za ta karbi bakuncin Arsenal ranar Lahadi, sannan ta kara da Newcastle United a Old Trafford a ranar Laraba. Ranar 19 ga watan Mayu, ne United za ta buga wasan karshe a bana a Premier League, wadda za ta je gidan Brighton kuma damar da ta rage a United domin kai wa gasar Zakarun Turai ta badi ita ce ta kammala kakar bana a mataki na shidan teburi, sai ta samu zuwa Europa Conference League.

 Haka kuma Manchester United za ta buga wasan karshe a FA Cup ranar 25 ga watan Mayu, idan ta dauki kofin zai ba ta damar shiga Europa League kai tsaye ta badi ko da a ce bata karkare a mataki na shida ba.

Shin Ya kamata A Kori Ten Hag?

Wasu suna ganin ya kamata shugabannin kungiyar su kori mai koyarwa Erik ten Hag saboda yadda yake jagorantar kungiyar akwai rashin kwarewa da kuma rashin salon buga wasa da ake bukata.

Amma kuma a duk lokacin da ya yi hira da manema labarai yana fakewa da cewa ‘yan wasan kungiyar suna yawan zuwa ciwo wanda hakan ne yasa baya samun cikakkun ‘yan wasan da za su bashi abin da yake so.

A wannan kakar kawai ‘yan wasan kungiyar sun samu Rauni kala-kala har sau 60, adadin da ba a taba samu ba a kan wata kungiya wanda hakan ya sa wasu suke ganin ba karamin kalubale bane ga shi mai koyarwa da ragowar masu taimaka masa da ma su kansu ‘yan wasan.

Sannan banda ciwo akwai matsaloli wadanda ba na cikin fili ba kamar rikicin shi kansa mai koyarwar da dan wasa Jadon Sancho da matsalar dan wasa Mason Greenwood da kuma matsalar nuna halin rashin da’a da dan wasa Marcus Rashford ya nuna a kwanakin baya.

A duk lokacin da aka yi masa tambaya a kan makomarsa, mai koyarwa Erik ten Hag yana cewa shi ne zai ci gaba da koyar da kungiyar har zuwa kakar wasa mai zuwa wanda hakan ba karamin kwarin gwiwa ya samu ba daga masu gudanarwa.

Sai dai duk da haka wasu suna ganin ba zai iya dawo da kungiyar hayyacinta ba domin bashi da kwarewar rike kungiya kamar Manchester United sannan suna ganin ya zama wajibi kungiyar ta shiga kasuwa domin neman masu koyarwa saboda ta maye gurbinsa.

Yanzu dai saura wasanni uku Manchester United ta kammala buga wasannin gasar firimiya inda za ta kece raini da Arsenal da Newcastle United da kuma kungiyar Brighton Albion sai kuma wasan karshe na gasar cin kofin kalubale na FA Cup da za su kece raini da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City a ranar 25 ga wannan watan a filin wasa na Wembley dake Birnin London.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Erik Ten HagKoraManchester United
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Gombe Za Ta Rungumi Shirin Farfado Da Noman Auduga Na Gwamnatin Tarayya – Inuwa

Next Post

Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

3 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

7 days ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa

Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa

LABARAI MASU NASABA

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.