ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Sin

Ziyarar aiki da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya kai kasar Faransa bisa gayyatar shugaban kasar, Emmanuel Macron, ta sake bayyana wa duniya kyakkyawan kudirin kasar Sin na kyautata alaka da duk kasashen duniya domin daidaita al’amuran da samun ci gaba mai dorewa a tafarkin zaman lafiya ba tare da zubar da jinin ko da dan tsako ba.

Kowa ya san irin taratsi da hargitsin da kasashen yamma suka jefa duniya a ciki inda a yau kusan a kowace kusurwa ana samun tashe-tashen hankula ko dai da makami ko kuma da mukami. Amma kuma ziyarar ta Shugaba Xi a Faransa wacce ta zo a bana da Jamhuriyar al’ummar kasar Sin ke cika shekara 75 da kafuwa ta kara aike sakon cewa ana iya yin aiki tare don cimma kyawawan manufofi na ciyar da dan Adam gaba.

Daga mukalar da Shugaba Xi ya rubuta aka wallafa a fitacciyar jaridar nan ta Faransa, Le Figaro, ya jaddada kudirin kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen duniya da zurfafa hadin kai da Faransa har ma da sauran kasashe domin a gudu tare a tsira tare. Wannan a fili yana nuna wa duniya cewa kasar Sin ba ta rowar kaifin basira da hikimomin da ta yi amfani da su wajen zama kasa ta biyu mafi girman tattalin arziki tare da tsame daruruwan miliyoyin mutanen karkara daga kangin talauci. Kuma bisa bunkasar tattalin arzikin da ta samu a bara da kashi 5.2 da kuma hasashen samun na bana da kashi 5 cikin 100, Sin tana mika goron gayyata ga kowa da kowa ya zo ya ci gajiyar damarmakin da ke kasar, kasancewar kasar za ta ci gaba da zama turbar ciyar da duniya gaba.

ADVERTISEMENT

Ba da wasa kasar Sin take zancen bude kofarta ba, misalin da Shugaba Xi ya bayar kan haka shi ne, “Muna maraba da karin kayayyakin amfanin gona da kayan kwalliya na kasar Faransa zuwa kasuwannin kasar Sin don biyan bukatun jama’ar kasar Sin da ke ci gaba da karuwa don samun ingantacciyar rayuwa. Muna maraba da saka hannun jari daga kamfanonin Faransa da na sauran kasashe a kasar Sin. Yanzu haka, mun bude kofar sashen masana’antun sarrafa kaya na kasar Sin gaba daya, kuma za mu hanzarta fadada hanyoyin shiga kasuwar sashen sadarwa, da likitanci da sauran ayyuka. Har ila yau, muna da wani shiri na dauke biza na kwanaki 15 ga baki daga kasashe da yawa ciki har da Faransa, kuma mun dauki karin matakai don saukaka tafiye-tafiye da biyan kudin baki a kasar Sin.”

Kasar Sin ba ta tsaya nan, tana ci gaba da karfafa gwiwar kamfanonin kasar su fadada ayyukansu zuwa kasashen duniya. A karkashin wannan, akwai kamfanonin kasar sama da 10,000 a Afirka da ke gudanar da aikace-aikace daban-daban musamman a karkashin kawancen Dandalin FOCAC.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Kasar Sin tana kara mara baya ga kamfanoninta su ci gaba da zuba jari a kasashen waje domin cin moriyar juna, a kan haka ne Shugaba Xi ya yi fatan Faransa za ta tabbatar da cewa kamfanonin Sin suna samun adalci wajen gudanar da kasuwancinsu daidai-wa-daida.

Wani abu mai muhimmanci da Shugaba Xi Jinping ya yi tsokaci a kai a mukalar tasa shi ne yadda kasar Sin za ta karfafa cudanya da hadin gwiwa da Faransa don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.
A bana an cika shekaru 70 da kafa ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana. Shekaru 70 da suka wuce, tsohon firaministan kasar Sin marigayi Zhou Enlai ya gabatar da cikakkun ka’idojin guda biyar a karon farko, sun kunshi “mutunta mulkin kai da cikakkun yankunan kasa na juna, da rashin cin zarafi a tsakanin juna, da rashin tsoma baki a cikin harkokin cikin gidan juna, da zaman daidaito da cin moriyar juna, da zaman tare cikin lumana”.

A tsawon wadannan shekaru, kasar Sin da magabatanta sun nuna muhimmancin rungumar zaman lafiya a duniya har ta kai ga ka’idojin nan guda biyar sun samu gagarumar karbuwa tare da aiki da su wajen tafiyar da dangantakar kasashen duniya a zamanance.

Saboda amannar da kasar Sin ta yi da zaman lafiya da mutunta juna, a sama da shekaru 70 da ta yi da kafuwa, ba ta taba takalar yaki ko mamaye ko da taku daya na yankin wata kasar waje ba. Kasar Sin ita ce kasa daya tilo a duniya da ta shigar da batun tsayawa tsayin daka kan hanyar bunkasa zaman lafiya a cikin kundin tsarin mulkinta, kana ita ce kadai daga cikin manyan kasashe masu makaman nukiliya da ta kuduri aniyar kin fara amfani da makaman nukiliya.

A aikace, kasar Sin ta kasance a sahun gaba wajen ganin an samar da dawwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya. Ta nemi a kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza kuma ta sha nuna goyon baya a kan samar da kasashe biyu masu cin gashin kansu a tsakanin Palasdinu da Isra’ila kamar yadda kudirin Majalisar Dinkin Duniya ya tanadar. Bugu da kari, Sin na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen warware rikicin Ukraine da Rasha ta hanyar lalama da kuma nunar wa kasashen duniya illolin da wadannan fitintinun suke haifarwa ga duniya.

A gaskiya, da za a yi cikakkiyar aiwatar da muhimman shawarwari guda uku da Shugaba Xi ya gabatar a ’yan shekarun nan a kan samar da wasu tsare-tsare na ci gaban duniya, da samar da tsaro da kuma wayewa daidai da zamanin da muke ciki wadda suka samu goyon baya da amincewar fiye da kasashe 100, tabbas za mu yi bankwana da bankwana da duk matsalolin da suka yi wa duniya kamun kazar kuku.

Sin
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.