ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Sin

Ziyarar aiki da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya kai kasar Faransa bisa gayyatar shugaban kasar, Emmanuel Macron, ta sake bayyana wa duniya kyakkyawan kudirin kasar Sin na kyautata alaka da duk kasashen duniya domin daidaita al’amuran da samun ci gaba mai dorewa a tafarkin zaman lafiya ba tare da zubar da jinin ko da dan tsako ba.

Kowa ya san irin taratsi da hargitsin da kasashen yamma suka jefa duniya a ciki inda a yau kusan a kowace kusurwa ana samun tashe-tashen hankula ko dai da makami ko kuma da mukami. Amma kuma ziyarar ta Shugaba Xi a Faransa wacce ta zo a bana da Jamhuriyar al’ummar kasar Sin ke cika shekara 75 da kafuwa ta kara aike sakon cewa ana iya yin aiki tare don cimma kyawawan manufofi na ciyar da dan Adam gaba.

Daga mukalar da Shugaba Xi ya rubuta aka wallafa a fitacciyar jaridar nan ta Faransa, Le Figaro, ya jaddada kudirin kasar Sin na kara bude kofarta ga kasashen duniya da zurfafa hadin kai da Faransa har ma da sauran kasashe domin a gudu tare a tsira tare. Wannan a fili yana nuna wa duniya cewa kasar Sin ba ta rowar kaifin basira da hikimomin da ta yi amfani da su wajen zama kasa ta biyu mafi girman tattalin arziki tare da tsame daruruwan miliyoyin mutanen karkara daga kangin talauci. Kuma bisa bunkasar tattalin arzikin da ta samu a bara da kashi 5.2 da kuma hasashen samun na bana da kashi 5 cikin 100, Sin tana mika goron gayyata ga kowa da kowa ya zo ya ci gajiyar damarmakin da ke kasar, kasancewar kasar za ta ci gaba da zama turbar ciyar da duniya gaba.

ADVERTISEMENT

Ba da wasa kasar Sin take zancen bude kofarta ba, misalin da Shugaba Xi ya bayar kan haka shi ne, “Muna maraba da karin kayayyakin amfanin gona da kayan kwalliya na kasar Faransa zuwa kasuwannin kasar Sin don biyan bukatun jama’ar kasar Sin da ke ci gaba da karuwa don samun ingantacciyar rayuwa. Muna maraba da saka hannun jari daga kamfanonin Faransa da na sauran kasashe a kasar Sin. Yanzu haka, mun bude kofar sashen masana’antun sarrafa kaya na kasar Sin gaba daya, kuma za mu hanzarta fadada hanyoyin shiga kasuwar sashen sadarwa, da likitanci da sauran ayyuka. Har ila yau, muna da wani shiri na dauke biza na kwanaki 15 ga baki daga kasashe da yawa ciki har da Faransa, kuma mun dauki karin matakai don saukaka tafiye-tafiye da biyan kudin baki a kasar Sin.”

Kasar Sin ba ta tsaya nan, tana ci gaba da karfafa gwiwar kamfanonin kasar su fadada ayyukansu zuwa kasashen duniya. A karkashin wannan, akwai kamfanonin kasar sama da 10,000 a Afirka da ke gudanar da aikace-aikace daban-daban musamman a karkashin kawancen Dandalin FOCAC.

LABARAI MASU NASABA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

Kasar Sin tana kara mara baya ga kamfanoninta su ci gaba da zuba jari a kasashen waje domin cin moriyar juna, a kan haka ne Shugaba Xi ya yi fatan Faransa za ta tabbatar da cewa kamfanonin Sin suna samun adalci wajen gudanar da kasuwancinsu daidai-wa-daida.

Wani abu mai muhimmanci da Shugaba Xi Jinping ya yi tsokaci a kai a mukalar tasa shi ne yadda kasar Sin za ta karfafa cudanya da hadin gwiwa da Faransa don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.
A bana an cika shekaru 70 da kafa ka’idoji biyar na zaman tare cikin lumana. Shekaru 70 da suka wuce, tsohon firaministan kasar Sin marigayi Zhou Enlai ya gabatar da cikakkun ka’idojin guda biyar a karon farko, sun kunshi “mutunta mulkin kai da cikakkun yankunan kasa na juna, da rashin cin zarafi a tsakanin juna, da rashin tsoma baki a cikin harkokin cikin gidan juna, da zaman daidaito da cin moriyar juna, da zaman tare cikin lumana”.

A tsawon wadannan shekaru, kasar Sin da magabatanta sun nuna muhimmancin rungumar zaman lafiya a duniya har ta kai ga ka’idojin nan guda biyar sun samu gagarumar karbuwa tare da aiki da su wajen tafiyar da dangantakar kasashen duniya a zamanance.

Saboda amannar da kasar Sin ta yi da zaman lafiya da mutunta juna, a sama da shekaru 70 da ta yi da kafuwa, ba ta taba takalar yaki ko mamaye ko da taku daya na yankin wata kasar waje ba. Kasar Sin ita ce kasa daya tilo a duniya da ta shigar da batun tsayawa tsayin daka kan hanyar bunkasa zaman lafiya a cikin kundin tsarin mulkinta, kana ita ce kadai daga cikin manyan kasashe masu makaman nukiliya da ta kuduri aniyar kin fara amfani da makaman nukiliya.

A aikace, kasar Sin ta kasance a sahun gaba wajen ganin an samar da dawwamammen zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya. Ta nemi a kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza kuma ta sha nuna goyon baya a kan samar da kasashe biyu masu cin gashin kansu a tsakanin Palasdinu da Isra’ila kamar yadda kudirin Majalisar Dinkin Duniya ya tanadar. Bugu da kari, Sin na ci gaba da taka muhimmiyar rawa wajen warware rikicin Ukraine da Rasha ta hanyar lalama da kuma nunar wa kasashen duniya illolin da wadannan fitintinun suke haifarwa ga duniya.

A gaskiya, da za a yi cikakkiyar aiwatar da muhimman shawarwari guda uku da Shugaba Xi ya gabatar a ’yan shekarun nan a kan samar da wasu tsare-tsare na ci gaban duniya, da samar da tsaro da kuma wayewa daidai da zamanin da muke ciki wadda suka samu goyon baya da amincewar fiye da kasashe 100, tabbas za mu yi bankwana da bankwana da duk matsalolin da suka yi wa duniya kamun kazar kuku.

Sin
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba
Ra'ayinmu

Kisan Gillar Marabar Jos: Bai Kamata Jinin Malama Ummulkhairi Ya Tafi A Banza Ba

July 3, 2026
sikila
Ra'ayinmu

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Next Post
Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.