• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba A Yi Hadin Gwiwa Domin Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sauyin yanayi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar dai yadda masana kan ce duniya gida ne guda ga daukacin bil adama, ta yadda abun da ya samu wani bangare na duniya na iya yin tasiri zuwa ga sauran sassan ta, haka abun yake game da batun sauyin yanayi. Mun dai ga yadda a shekarun baya bayan nan tasirin sauyin yanayi ke haifar da bala’u iri daban daban a bangarorin duniya mabanbanta.

Sassan kasashe daban daban na fuskantar ibtila’in fari, da ambaliyar ruwa, da kwararar hamada, da matukar karuwar zafi irin wanda kan hallaka nau’o’in halittu daban daban dake rayuwa a doron wannan duniya.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani

A cewar masana, watan da ya gabata, ya kasance Agusta mafi zafi, da masu binciken kimiyya suka tantance ta amfani da na’u’rorin zamanin yau, kuma watan Yulin da ya gaba ne kadai ya fi shi zafi bisa alkaluman da aka tattara.

Bisa wannan sakamako ne ma babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi gargadin cewa, yanayin duniyar mu na kara tabarbarewa, inda a bana duniya ta yi fama da garjin-rana mai matukar kuna, wanda ya zamo mafi zafi a tarihi.

A bangaren masana, dake ba da shawarar hanyoyin tunkarar wannan kalubale kuwa, da yawa na cewa tuni lokaci ya yi na daukar matakai tare, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. Wannan shawara na nufin jagorori a matakai daban daban, su zabura wajen aiwatar da matakan gaggawa bisa hadin gwiwa, domin yayyafawa wannan matsala ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

A halin da ake ciki yanzu, duniya ba ta da lokacin jira, ko na batawa. Don haka muna iya cewa, matakan tarukan kasa da kasa, kamar taron sauyin yanayi na MDD wanda za a gudanar a karshen watan nan na Satumba a birnin New York, da taron COP28 na watan Nuwamba a hadaddiyar daular larabawa, da ma wanda ya gudana a Kenya a baya bayan nan da makamantan su, sun zo a kan gaba. To sai dai kuma, duniya ta fi bukatar matakai na zahiri na cimma wannan buri, irin su cika alkawuran da manyan kasashen duniya suka jima suna yi, na samar da kudade, da kwarewar makamar aiki, da hadin gwiwa kai tsaye tare da kasashe masu rauni da masu tasowa, ta yadda za a kai ga cin gajiyar matakan kimiyya da fasahohin zamani, na shawo kan sauyin yanayin nan dake addabar dukkanin duniya baki daya.

 

.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Marawa AU Baya Wajen Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Next Post

Gwamnatin Nijeriya Ta Dakatar Da Aikin Hanyoyi A Yankin Kudu Maso Gabas

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

20 hours ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

21 hours ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

22 hours ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

23 hours ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Gwamnatin Nijeriya Ta Dakatar Da Aikin Hanyoyi A Yankin Kudu Maso Gabas

Gwamnatin Nijeriya Ta Dakatar Da Aikin Hanyoyi A Yankin Kudu Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 

August 10, 2025
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

August 10, 2025
Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.