ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Wajaba A Yi Hadin Gwiwa Domin Shawo Kan Kalubalen Sauyin Yanayi 

by CMG Hausa
3 years ago
Sauyin yanayi

Kamar dai yadda masana kan ce duniya gida ne guda ga daukacin bil adama, ta yadda abun da ya samu wani bangare na duniya na iya yin tasiri zuwa ga sauran sassan ta, haka abun yake game da batun sauyin yanayi. Mun dai ga yadda a shekarun baya bayan nan tasirin sauyin yanayi ke haifar da bala’u iri daban daban a bangarorin duniya mabanbanta.

Sassan kasashe daban daban na fuskantar ibtila’in fari, da ambaliyar ruwa, da kwararar hamada, da matukar karuwar zafi irin wanda kan hallaka nau’o’in halittu daban daban dake rayuwa a doron wannan duniya.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani

A cewar masana, watan da ya gabata, ya kasance Agusta mafi zafi, da masu binciken kimiyya suka tantance ta amfani da na’u’rorin zamanin yau, kuma watan Yulin da ya gaba ne kadai ya fi shi zafi bisa alkaluman da aka tattara.

ADVERTISEMENT

Bisa wannan sakamako ne ma babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya yi gargadin cewa, yanayin duniyar mu na kara tabarbarewa, inda a bana duniya ta yi fama da garjin-rana mai matukar kuna, wanda ya zamo mafi zafi a tarihi.

A bangaren masana, dake ba da shawarar hanyoyin tunkarar wannan kalubale kuwa, da yawa na cewa tuni lokaci ya yi na daukar matakai tare, ta yadda za a gudu tare a tsira tare. Wannan shawara na nufin jagorori a matakai daban daban, su zabura wajen aiwatar da matakan gaggawa bisa hadin gwiwa, domin yayyafawa wannan matsala ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

A halin da ake ciki yanzu, duniya ba ta da lokacin jira, ko na batawa. Don haka muna iya cewa, matakan tarukan kasa da kasa, kamar taron sauyin yanayi na MDD wanda za a gudanar a karshen watan nan na Satumba a birnin New York, da taron COP28 na watan Nuwamba a hadaddiyar daular larabawa, da ma wanda ya gudana a Kenya a baya bayan nan da makamantan su, sun zo a kan gaba. To sai dai kuma, duniya ta fi bukatar matakai na zahiri na cimma wannan buri, irin su cika alkawuran da manyan kasashen duniya suka jima suna yi, na samar da kudade, da kwarewar makamar aiki, da hadin gwiwa kai tsaye tare da kasashe masu rauni da masu tasowa, ta yadda za a kai ga cin gajiyar matakan kimiyya da fasahohin zamani, na shawo kan sauyin yanayin nan dake addabar dukkanin duniya baki daya.

 

.

Sauyin yanayi
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola
Daga Birnin Sin

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Nijeriya Ta Dakatar Da Aikin Hanyoyi A Yankin Kudu Maso Gabas

Gwamnatin Nijeriya Ta Dakatar Da Aikin Hanyoyi A Yankin Kudu Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.