• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Sallar Idi A Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya tare da Sarkin Gombe, Alhaji (Dakta) Abubakar Shehu Abubakar III, gami da dubban al’ummar musulmai ne suka gudanar da Sallar Idi mai raka’a biyu a jihar da ke alamta kammala Azumin watan Ramadana.

Mataimakin babban limamin Gombe, Ustaz Aliyu Hammari, shi ne ya jagoranci Sallar wacce ta hada fuskokin dubban jama’a da jami’an gwamnati, kakakin majalisar jihar da sauransu.

  • Sakon Sallah: Gwamna Nasir Ya Yi Kira Da Hadin Kai Don Gina Jihar Kebbi
  • Gidauniyar Saraki Ta Kammala Shirin Rabon Abincin Buda-baki

Kazalika, bayan kammala Sallar Idin an gudanar da hawan sallah cikin kasaita da kyale-kyale domin nuna murna da farin ciki da wannan Idin.

A sakonsa na sallah ga al’ummar musulmai, Gwamnan Jihar Gombe, kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa Muhammadu Inuwa Yahaya ya taya al’ummar Musulmin jihar murnar bikin Sallar Idi, yayin da suka bi sahun takwarorinsu na faɗin duniya don alamta ƙarshen azumin watan Ramadan mai alfarma.

A sakonsa na fatan alheri dauke da sanya hannun kakakinsa Malam Ismaila Uba Misilli, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmai su kiyaye koyarwa da dabi’un da suka koya a cikin watan na Ramadan, tare da ɗabbaƙasu a cikin rayuwarsu ta yau da kullum don ci gaban al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Gombe

Ya jawo hankalin al’ummar jihar wajen yin addu’o’in hadin kai da juriya a tsaka da kalubalen tattalin arziki da ake fama da shi, inda ya tabbatar da cewa matsalolin da ake fama da su a halin yanzu masu wucewa ne, yana mai cewa Nijeriya za ta farfaɗo daga wadannan matsaloli.

Gwamnan ya kuma bukaci al’ummar Musulmi su ci gaba da dabbaƙa ibadun da suka gudanar a cikin watan mai alfarma tare da dorar da darussan da aka koya a yayin tafsirai don ci gaban addini, da al’umma baki ɗaya, yana mai jaddada cewa Nijeriya tana matukar bukatar mutanen kirki, masu kyawawan halaye don shawo kan munanan ayyukan da wasu ‘yan tsirarun da ba sa nufin kasar da alheri suka haddasa.

Shugaban kungiyar gwamnonin na Arewa ya kuma jaddada mahimmancin kyawawan dabi’u wajen yakar matsalolin al’umma.

Ya ce, “Wannan lokaci na sallar idi yana nuni da sadaukarwa, kauna da biyayya ga rukunan Musulunci. Don haka ina yi mana wasiyya da mu dabbaƙa darussan da muka koya a wannan wata na Ramadan da nuna kauna ga juna tare da inganta zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu daban-daban”.

“Kamar yadda dukkanmu muka tuna da marassa galihu da talakawa a cikin watan na Ramadan, ina rokonmu mu ci gaba da wadannan dabi’u har bayan Ramadan.”

Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na wanzar da zaman lafiya da tsaro, inda ya sha alwashin cewa gwamnatin ba za ta amince da duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiyan da ake mora a jihar ba.

Da yake jaddada muhimmancin samar da romon demokradiyya, ya bai wa al’ummar jihar tabbacin cewa gwamnatinsa tana mai da hankali wajen nausa jihar da al’ummarta gaba.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ja hankalin al’ummar jihar su yi amfani da wasu tsare-tsaren da gwamnatin tarayya da ta jihar suka bullo da su don bunkasa tattalin arzikinsu.

Gombe

Ya kuma bayyana muhimmancin noma wajen bunkasa tattalin arziki da tabbatar da samar da abinci, inda ya bukaci jama’a su yi amfani da damar da za su samu a harkar noma, tare da karkata akalarsu ga sana’o’i masu nagarta, yana mai bayyana kwarin guiwarsa kan al’ummar Jihar ta Gombe.

Ya yi kira ga sarakunan gargajiya, malaman addini, da shugabannin al’umma su ci gaba da bai wa gwamnati goyon baya wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro don ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin jihar, yana mai tabbatar da aniyarsa ta aiwatar da ayyukan raya kasa da tsare-tsaren bunkasa jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Sin Za Ta Ci Gaba Da Shiga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Next Post

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Related

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

4 minutes ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

4 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

6 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

6 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

7 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

10 hours ago
Next Post
Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

Shigar Da Japan Cikin AUKUS Kara Kuskure Manufar Kungiyar Ce

LABARAI MASU NASABA

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.