• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Shafe Shekara 14 Ba A Biya Tsofaffin Ma’aikata Fansho Da Kudin Sallama A Adamawa Ba

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Aka Shafe Shekara 14 Ba A Biya Tsofaffin Ma’aikata Fansho Da Kudin Sallama A Adamawa Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Tsoffin Ma’aikata ta Kasa (NUP) a Jihar Adamawa, ta koka kan yadda aka kwashe shekara tara zuwa 14, ba tare da gwamnatin jihar ta biya tsofaffin ma’aikata kudin sallama ba.

Shugaban Kungiyar Tsofaffin Ma’aikata ta jihar, Muhammad Sali ne, ya bayyana haka ga manema labarai a Yola.

  • Hajji 2023: Alhazan Jihar Kwara 272 Sun Dawo Gida Nijeriya
  • Bidiyon Dala: Gwamnatin Kano Ta Fara Bincike Akan Ganduje

Sali, ya ce shekaru da dama gwamnatin jihar ta gaza biyan tsofaffin ma’aikatan kudaden da su ke bi bashi.

Ya kara da cewa “Shekaru tara gwamnati ta gaza sallamar tsofaffin ma’aikatan jiha, shekara 14 ba ta biya kudaden sallamar tsofaffin ma’aikatan kananan hukumomin jihar ba, duk da alkawarin da mai girma gwamna ya yi mana,” in ji Sali.

Da yake magana game da kudaden fansho da gwamnatin ke biyan tsofaffin ma’aikatan duk wata, shugaban kungiyar yac e “da ban mamaki har yanzu mafi karancin fansho shi ne 4000, kana da shekaru 60, kana karbar dubu hudu ko kudin magani ba zai maka ba.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Gwamnatin jihar na biyan dubu 32 mafi karancin albashi, bisa doka dubu 25 za a biya a matsayin mafi karancin fansho a wata, amma mu har yanzu dubu hudu ake ba mu.

“Doka ne, ko an kara albashi ko ba a kara ba, duk shekara biyar ana kara kudin fansho, amma mu an kara albashin ba a kara mana ba, muna rokon mai girma gwamna da ya duba wannan batu.

“Kullum mambobin kungiyarmu mutuwa suke duk da akwai wa’adi, amma rashin samun yadda za a kula da kai da matsalolin rayuwa ke kashe da dama a cikinmu,” in ji Sali.

Kazalika, ya ce kungiyar mai mambobi dubu takwas a jihar, tun 2013 da aka biya su ba a sake biyan tsofaffin ma’aikatan kudaden sallama ba.

Don haka ya jaddada rokonsa ga gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, da ya yi wani abu domin ceto rayuwar tsofaffin ma’aikatan.

Haka kuma shugaban ya shawarci mambobin kungiyar da su ci gaba da hakuri zuwa lokacin da gwamnan zai share musu hawaye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaFanshoKudin SallamaKungiyar Tsofaffin Ma'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajji 2023: Alhazan Jihar Kwara 272 Sun Dawo Gida Nijeriya

Next Post

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

4 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

5 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
Fansho
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

10 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

11 hours ago
Next Post
Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.