ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin: Bai Kamata Japan Ta Dauki Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zuba Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba

by CMG Hausa
3 years ago
空撮 東京電力福島第一原発/処理水の海洋放出に向けて準備が進む東京電力福島第一原発=2023年7月4日午前10時52分、朝日新聞社ヘリから=福島県

空撮 東京電力福島第一原発/処理水の海洋放出に向けて準備が進む東京電力福島第一原発=2023年7月4日午前10時52分、朝日新聞社ヘリから=福島県

Kasar Sin ta ce bai kamata kasar Japan ta dauki rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) ta fitar a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba, tana mai bukatar Japan din ta hada hannu da hukumar IAEA wajen samar da wani tsarin sa ido na kasa da kasa, mai dogon zango.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan a lokacin da aka nemi ya yi tsokaci kan rahoton, wanda ya yi amana shirin Japan na zuba dagwalon nukiliya cikin teku ya dace da matakan aminci na kasa da kasa. Yana mai cewa, IAEA za ta dauki lokaci mai tsawo tana sa ido kan ayyukan Japan.
A cewar kakakin, an gano rahoton ya gaza bayyana cikakken ra’ayoyin masanan da suka nazarci shirin, haka kuma ba a sanar da dukkanin masanan sakamakon nazarin ba.

  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa Wajen Kare Mabanbantan Wayewar Kan Al’umma

Yana mai cewa, kasar Sin na takaicin gaggawar da aka yi wajen fitar da rahoton.
Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya maida martani kan rahoton hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA, na tantance aikin zubar da dagwalon ruwan nukiliyar kasar Japan cikin teku, inda ya jaddada cewa, bai kamata Japan ta dauki rahoton a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba.

ADVERTISEMENT

Wang ya nuna cewa, rahoton ba ya shaida amincin shirin Japan, na juye dagwalon ruwan nukiliyar ta cikin teku, kana kuma, ba zai iya tabbatar da tsaron aikin ba. Jami’in ya jaddada cewa, juye dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, zai illata babbar moriyar kasa da kasa, don haka bai kamata a kuskure fahimtar hakan ba.

Game da batun, mai fashin baki yana mai cewa, bayan da ya duba rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya wato IAEA ya fitar jiya Talata 4 ga wata, wanda ya yi duba kan yunkurin kasar Japan na zubar da dagwalon ruwan nukiliya cikin teku, babban jami’in kungiyar masu aikin su ta jihar Miyagi-ken ta kasar, Terazawa Haruhiko ya nuna damuwa sosai. Kamar yadda yake nuna damuwa kan hakan, jama’ar kasar Japan da dama suna ganin cewa, abun da rahoton ya bayyana, cewa wai shirin juye dagwalon ruwan nukiliya cikin teku na Japan, ya dace da ma’aunin tsaro na kasa da kasa, ba mai gamsarwa ba ne. Har ma kungiyoyin da ba na gwamnati ba da dama a kasar Koriya ta Kudu sun ce, bai dace rahoton ya zama dalilin Japan na juye dagwalon ruwan nukiliya cikin tekun ba.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Saboda rahoton bai bayyana ra’ayoyin dukkan kwararrun da suka halarci aikin tantancewa ba, kuma sakamakon rahoton bai samu amincewa ta bai daya daga dukkan kwararrun ba.

Idan aka dubi ayyukan da kasar Japan take yi kwanan nan, akwai abubuwan shakku sosai a ciki. Mu dauki kasafin kudin hukumar farfado da kasar ta Japan na shekara ta 2021 a matsayin misali, kasafin kudin da ya shafi shawo kan tasirin hadarin makamashin nukiliya a tashar Fukushima ya karu zuwa kudin Japan Yen biliyan 2, wanda ya ninka har sau 4 idan aka kwatanta da na shekara ta 2020. Haka kuma, kafafen watsa labaran Koriya ta Kudu sun ce, kafin hukumar IAEA ta bullo da rahoton, gwamnatin Japan ta riga ta samu daftarin sa, har ma ta gabatar da ra’ayoyin gyaran shi.

Bugu da kari, an ce, jami’an gwamnatin Japan sun baiwa jami’an hukumar IAEA kyautar kudade da yawansu ya zarce EURO miliyan 1. Idan da gaske ne hakan, to, ina dalilin da ya sa gwamnatin Japan ta kashe wadannan kudade tare da yin irin wannan kokari?
Ba za’a iya amincewa da yunkurin gwamnatin Japan, na zubar da dagwalon ruwan nukiliya sama da ton miliyan 1 zuwa tekun Pasifik a cikin nan da shekaru 30 masu zuwa ba. Zabin Japan na zubar da shi kai-tsaye domin cimma muradun kanta, kawai haifar da hadari ne za ta yi, ga daukacin al’ummun duniya. (Masu Fassarawa: Fa’iza Mustapha, Murtala Zhang)

Kasar sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Bayan Kin Gaskiya…

Bayan Kin Gaskiya…

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.