• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Al’umma Za Su Taimaka Wa Makarantu

byIdris Aliyu Daudawa
2 years ago
Makarantu

A duk Unguwa, Gari, ko wani babban Birni da akwai wadansu mutane da turanci ana kiransu school board management committee ba karamar gudunmawa suke badawa ba wajen tabbatar da cewa makarantu suna tafiyar da harkokinsu na ayyukansu kamar yadda ya dace. Suna taimakawa ne wajen ganin makarantu suna tafiyar da ayyukansu ba tare da shiga wata matsala ba.Bugu da kari kuma su kungiya ce mai zaman kanta wadda take wakiltar al’umman makaranta da suka hada da, ‘yan makaranta, Malamai, Iyaye,Kungiyar Iyaye da Malamai, Shugabannin al’umma, har ma da sauran wadanda suke da sha’wa a kan al’amarin daya shafi ilimi.

‘Yan makaranta su gudunmawar da za su bada a nasu matsayin na dalibai shi ne su kasance masu bin dokokin da makaranta ta shimfida,ta yin amfani da su saboda yin hakan ne zai kasance sun tashi cikin da’a da maida hankali ga abubuwan da ake koya masu ta darussa cikin aji tare da wasu dabi’u wadanda za su zamar masu tamkar abokansu.Domin suma suna son watarana ace sun zama mutanen kwarai.

  • Bikin Bazara Da Ke Fadada A Duniya Alama Ce Ta Mu’amala Da Fahimtar Juna Tsakanin Wayewar Kan Kasar Sin Da Wayewar Kai Daban-Daban
  • Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta

Malamai su a kowane lokaci ana son su kasance baya ga ilimin da suke da shi wanada za su koyawa dalibai ta hanyar darussa abin da ya kasance kowa daga cikinsu yana da darasin da yake koyawa, dabi’unsu su zama lalle abin koyi ne wadanda daliban nasu su rika koyi da su ta hanyar aikatawa.Malamai sun kwana da sanin duk wadansu abubuwan da za su rika yi a gaban dalibansu da suka zama akasin dabiu’u nagari ba za su haifar da da mai ido ba.Sun san da cewar sune makaranta ta biyu wajen samar da ilimi da tarbiyya bayan ta farko da Iyaye suka kasance Malamanta.

Iyaye sune makaranta ta farko wadanda da suke kasancewa wani babban ginshikin rayuwa gaba daya da su ‘ya’yansu wadanda su ne daliban, matsawar sun basu tarbiya ta gari a matsayinsu na makaranta ta farko wadda daga wurinsu ne za a fara dorasu kan tafarki nagari. Malaman makaranta ba za su fuskanci wata matsala mai yawa da har su daliban sun samu kyakkyawar tarbiya daga makaranta ta farko da Iyaye suka kasance Malamai.

Shugabannin al’umma wadannan sun hada da masu gari kamar Mai unguwa,Dagaci, Hakimi, ko Sarki da sauran manyan gari da suke da ruwa da zaki wajen ganin lalle makaranta tana tafiya kamar yadda duk makaranta yakamata. Suna yin haka ne wajen bada gudunmawa musamman ma wajen ganin makarantar bata fuskantar wata matsala da zata kawozama mata wani tarnaki wajen makarantar ta rika tafiya kafada- kafada kamar yadda sauran makarantu suke tafiyar da harkokinsu.

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

Kungiyar Iyaye da Malamai ba karamar gudunmawa kungiyar take badawa a makaranta ba wajen maganin duk wata matsala da ta yaso saboda sanin kowa ne,bayan ‘yanmakaranta sun baro gida zuwa makaranta har zuwa lokacin tashinsu suna tare ne da Malamai wadanda su suka san yadda suke fahimta ko gane ilimin da suke koya masu ta darussa daban-daban.Su suka fi kowa sanin irin kwazon yaran don haka sune suka fi kowa dacewa sanin kwazonsu a aji da irin halayensu.

Masu ruwa da tsaki su wadannan sun kasance ne dukwani abin da yake da nasaba da ilimi suna bayar da gudunmawa ne wannan kuma ba sai a garin da suke zama bane har ma wadanda ba garuruwan su bane na asali suna bada gudunmawa musamman ma ta bangaren ilimi domin sun san babban shine babban ginshiki na rayuwar al’umma ci gabansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
gaza

Majalisar Dattijai Ta Bukaci Cikakkun Bayanai Kan Kashe Kudaden Aikin Gas Na Naira Biliyan 100

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version