• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a kauyen Natsinta cikin karamar hukumar Jibiya da ke Jihar Katsina ya lalata gidaje kimanin 255, jim kadan bayan dauke ruwan sama.

Lamarin ya faruwa ne sakamakon ruwan sama da aka rika yi ba kaukautawa kwanaki a jere, wanda ya yi sanadiyar korar mutane fiye da dubu daya daga muhallinsu, wanda da yawansu mata ne da kananan yara.

  • PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Sai dai ba a samu labarin rasa rai ba, amma dai mutane da dama sun samu raunuka, wanda yanzu haka suna asibiti suna karbar magani.

Haka kuma mafiyancin gidajen da ruwa ya ruguje gidajen kasa ne wanda a dalilin haka jama’a da dama sun rasa matsugunnisu kuma suna bukatar taimakon gaggawa.

Mai unguwar garin Natsinta, Malam Dayyabu ya nuna fargaba kan faruwar wannan lamari, inda ya ce yanzu abin da ke gabansu shi ne, kokarin samun abin da za su sanya a bakin salati tun da ruwa ya hargitsa duk abubuwan da suke da shi.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

“Babu abin da zan ce sai dai mun gode Allah wanda ya kaddara faruwar wannan lamari kuma babu wanda ya isa tambayi dalilin me ya sa, ganin damarsa ce ya yi haka,” in ji mai unguwa.

A cewarsa, kimanin gidaje 250 iftila’i ya shafa, ba a maganar gidajen da ruwa ya kada a yau (Litinin), yanzu haka wasu karin gidaje guda 4 sun kara faduwa sannan kuma wasu guda biyu sun ruguje baki daya.

“Muna kira ga gwamnatin Jihar Katsina karkashin Gwamna Malam Dikko Umar Radda da su taimaka wa al’umma da kayayyakin rufi da katifu da siminti da bulo da kudadai domin su samu inda za su tsugunna su yi barci a yanzu, ” in ji shi.

Sai dai kuma dan majalisar dokoki mai wakiltar karamar hukumar Jibiya Honarabule Mustapha Yusuf ya ziyarci kauyen Natsinta domin jajanta masu da ganin irin barnar da ruwan ya yi, inda ya yi alkawari kai kokensu a gaban majalisa domin tattauna yadda gwamnati za ta tallafa wa wadanda wannan bala’i ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660

Next Post

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2 hours ago
Natsinta
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

4 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

10 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

10 hours ago
Next Post
Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa - Hon Boza

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Natsinta

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.