• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a kauyen Natsinta cikin karamar hukumar Jibiya da ke Jihar Katsina ya lalata gidaje kimanin 255, jim kadan bayan dauke ruwan sama.

Lamarin ya faruwa ne sakamakon ruwan sama da aka rika yi ba kaukautawa kwanaki a jere, wanda ya yi sanadiyar korar mutane fiye da dubu daya daga muhallinsu, wanda da yawansu mata ne da kananan yara.

  • PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Sai dai ba a samu labarin rasa rai ba, amma dai mutane da dama sun samu raunuka, wanda yanzu haka suna asibiti suna karbar magani.

Haka kuma mafiyancin gidajen da ruwa ya ruguje gidajen kasa ne wanda a dalilin haka jama’a da dama sun rasa matsugunnisu kuma suna bukatar taimakon gaggawa.

Mai unguwar garin Natsinta, Malam Dayyabu ya nuna fargaba kan faruwar wannan lamari, inda ya ce yanzu abin da ke gabansu shi ne, kokarin samun abin da za su sanya a bakin salati tun da ruwa ya hargitsa duk abubuwan da suke da shi.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu

“Babu abin da zan ce sai dai mun gode Allah wanda ya kaddara faruwar wannan lamari kuma babu wanda ya isa tambayi dalilin me ya sa, ganin damarsa ce ya yi haka,” in ji mai unguwa.

A cewarsa, kimanin gidaje 250 iftila’i ya shafa, ba a maganar gidajen da ruwa ya kada a yau (Litinin), yanzu haka wasu karin gidaje guda 4 sun kara faduwa sannan kuma wasu guda biyu sun ruguje baki daya.

“Muna kira ga gwamnatin Jihar Katsina karkashin Gwamna Malam Dikko Umar Radda da su taimaka wa al’umma da kayayyakin rufi da katifu da siminti da bulo da kudadai domin su samu inda za su tsugunna su yi barci a yanzu, ” in ji shi.

Sai dai kuma dan majalisar dokoki mai wakiltar karamar hukumar Jibiya Honarabule Mustapha Yusuf ya ziyarci kauyen Natsinta domin jajanta masu da ganin irin barnar da ruwan ya yi, inda ya yi alkawari kai kokensu a gaban majalisa domin tattauna yadda gwamnati za ta tallafa wa wadanda wannan bala’i ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660

Next Post

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Related

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

12 minutes ago
Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
Labarai

Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu

1 hour ago
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar
Labarai

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

2 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

4 hours ago
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

14 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

15 hours ago
Next Post
Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa - Hon Boza

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

Ƴansanda Sun Cafke Barayin Motoci 3 A Kano

July 28, 2025
Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu

Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu

July 28, 2025
An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar

July 28, 2025
Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya

July 28, 2025
Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.