• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina

by El-Zaharadeen Umar and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Yadda Ambaliya Ta Lalata Gidaje 255 A Garin Natsinta Da Ke Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya a kauyen Natsinta cikin karamar hukumar Jibiya da ke Jihar Katsina ya lalata gidaje kimanin 255, jim kadan bayan dauke ruwan sama.

Lamarin ya faruwa ne sakamakon ruwan sama da aka rika yi ba kaukautawa kwanaki a jere, wanda ya yi sanadiyar korar mutane fiye da dubu daya daga muhallinsu, wanda da yawansu mata ne da kananan yara.

  • PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660
  • Gwamnatin Kano Za Ta Tsara Zamantar Da Magungunan Gargajiya

Sai dai ba a samu labarin rasa rai ba, amma dai mutane da dama sun samu raunuka, wanda yanzu haka suna asibiti suna karbar magani.

Haka kuma mafiyancin gidajen da ruwa ya ruguje gidajen kasa ne wanda a dalilin haka jama’a da dama sun rasa matsugunnisu kuma suna bukatar taimakon gaggawa.

Mai unguwar garin Natsinta, Malam Dayyabu ya nuna fargaba kan faruwar wannan lamari, inda ya ce yanzu abin da ke gabansu shi ne, kokarin samun abin da za su sanya a bakin salati tun da ruwa ya hargitsa duk abubuwan da suke da shi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

“Babu abin da zan ce sai dai mun gode Allah wanda ya kaddara faruwar wannan lamari kuma babu wanda ya isa tambayi dalilin me ya sa, ganin damarsa ce ya yi haka,” in ji mai unguwa.

A cewarsa, kimanin gidaje 250 iftila’i ya shafa, ba a maganar gidajen da ruwa ya kada a yau (Litinin), yanzu haka wasu karin gidaje guda 4 sun kara faduwa sannan kuma wasu guda biyu sun ruguje baki daya.

“Muna kira ga gwamnatin Jihar Katsina karkashin Gwamna Malam Dikko Umar Radda da su taimaka wa al’umma da kayayyakin rufi da katifu da siminti da bulo da kudadai domin su samu inda za su tsugunna su yi barci a yanzu, ” in ji shi.

Sai dai kuma dan majalisar dokoki mai wakiltar karamar hukumar Jibiya Honarabule Mustapha Yusuf ya ziyarci kauyen Natsinta domin jajanta masu da ganin irin barnar da ruwan ya yi, inda ya yi alkawari kai kokensu a gaban majalisa domin tattauna yadda gwamnati za ta tallafa wa wadanda wannan bala’i ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

PCACC Ta Kama Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Bisa Zargin Almundahanar Miliyan 660

Next Post

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Related

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

53 minutes ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

4 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

13 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

14 hours ago
Next Post
Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa – Hon Boza

Martani: Ba Hannuna A Kisan Sarkin Gobir, Sharri Ne Na Ƴan Adawa - Hon Boza

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.