• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi

by Umar Faruk
8 months ago
in Labarai
0
Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi da Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), sun gudanar da bikin ranar yara ta duniya tare da yin kira ga yaran su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tashe-tashen hankula, da dabi’un marasa kyau.

Bikin wanda aka gudanar a Birnin Kebbi a ranar Laraba, wani kokari ne na hadin guiwa da AGILE da kungiyar masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke yekuwa kan ilimi.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Matatar Dangote Ta Fara Fitar Man Fetur Dinta Zuwa Kasashen Afrika

Bikin ya samu halartar makarantun sakandire guda 10 da suka halarci tarukan kacici-kacici da muhawara a wajen taron bikin.

Babban sakataren ma’aikatar yada labarai da al’adu, Alhaji Buhari Wara, ya nanata kudirin gwamnatin jihar na tallafa wa rayuwar yara ta hanyar ingantaccen ilimi da yanayin Karatu mai kyau.

Ya kuma jaddada cewa jihar na da burin samar wa yara damar samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, tsaftataccen ruwan sha, da muhalli mai kyau.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Hakazalika Alhaji Buhari Wara, ya bukaci yara su mayar da hankali kan karatunsu, su nisanci munanan dabi’u, su tabbatar da tsaron lafiyarsu.

“Yara su ne kashin bayan al’umma,” in ji Wara.

“Yayin da kuka girma, za ku fuskanci kalubale da yawa.

“Ku guje wa shaye-shayen kwayoyi, tashin hankali, da halayen da ba a so, yayin da suke haifar da mummunan sakamako.

“Saboda haka ku mayar da hankali kan karatunku, kuma za ku samu ikon zabar makomarku kuma ku samu hikima.”

Dokta Sahail Sheikh, wakilin UNICEF, ya jaddada sadaukarwar kungiyar wajen yi wa mata da yara hidima, tare da ba su damarmaki a fannoni daban-daban na rayuwa, da suka hada da kiwon lafiya, ilimi, tsaftataccen ruwan sha, hakkin yara, da kariya daga cututtuka masu yaduwa.

Ko’odinetan NYSC reshen Jihar Kebbi, Alhaji Bala Dabo, ya yaba wa Kungiyar UNICEF da Kungiyar CDS ta ilimi bisa shirya gasar kacici-kacici a tsakanin makarantu tare da hadin gwiwar UNICEF.

Kwalejin ‘yan mata da ke Makerar Gwandu ce ta zo na daya a gasar kacici-kacici da maki 60, sai Kwalejin Rayhaan da maki 55, sai makarantar Royal Lead academy da maki 40.

Taken ranar yara ta duniya na bana, “Kyakkyawan Ilimi Yana da Muhimmanci ga Al’umma,” a duk lokacin da aka gudanar da taron, dukkanin makarantun da suka halarci bikin ana ba su takardar shaidar halartar bikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BikiKebbiUNICEFYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Sakataren FEDECO, Ahmadu Kurfi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 93

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da ÆŠansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

7 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

10 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

11 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.