• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Fintiri Da Atiku Suka Gudanar Da Bikin Sallah A Adamawa

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Fintiri Da Atiku Suka Gudanar Da Bikin Sallah A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na Jihar Adamawa ya bi sahun dubban al’ummar musulmi a babban filin idi na tsakiyar birnin Yola domin gudanar da sallah.

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, Barista Auwal Tukur, manyan jami’an gwamnati, da shugabannin masana’antu suma sun halarci sallar.

  • Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
  • An Kashe Mutum 2, An Raunata 3 A Wani Sabon Hari A Filato

Bayan gudanar da sallar, Khadi Ahmadu Bobboi, babban limamin masallacin Modibbo Adamawa, ya gabatar da wa’azi mai taken tarihi da muhimmancin Idin Babbar Sallah ga al’ummar Musulmi.

Bobboi ya yi magana game da nau’o’in dabbobin da ake yankawa, ya kuma jaddada muhimmancin yanka dabbobi masu lafiya bisa hadisan Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam.

A cikin sakonsa na Sallah, Wazirin AdamWa Alhaji Atiku Abubakar ya taya al’ummar musulmi barka da Sallah tare da yi wa alhazan Adamawa da ke Saudiyya fatan gudanar da aikin Hajjin bana karbabbiya.

Labarai Masu Nasaba

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

Ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su ji tsoron Allah su koyi zama lafiya da ‘yan uwansu, inda ya bukaci gwamnatoci da shugabannin al’umma da su koya wa talakawansu dangantaka mai kyau da jituwa.

Ya nuna damuwarsa kan rashin fahimtar juna da ke ci gaba da wanzuwa tsakanin makiyaya da manoma a jihar, inda ya bukace su da su mutunta juna domin samun zaman lafiya.

Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta dauki matakin da ya dace a kan masu aikata laifin.

Ya gode wa Gwamna Umaru Fintiri bisa cika alkawuran da ya dauka na samar da ci gaba ga al’ummar jihar, ya kuma yi addu’ar Allah ya ba shi basira don ci gaba da ayyukan alheri a wa’adinsa na biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaAtikuFintiriSallah Babba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalibai Sun ‘Yantar Da Fursunoni 6 A Gidan Yarin Suleja

Next Post

Zaman Lafiya Zai Bunkasa A Kaduna -Uba Sani

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

49 minutes ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

2 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

14 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

14 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

16 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

18 hours ago
Next Post
Zaman Lafiya Zai Bunkasa A Kaduna -Uba Sani

Zaman Lafiya Zai Bunkasa A Kaduna -Uba Sani

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.