• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Adaidaita Sahu 650 Da Babura 1000 A Sokoto

Ya Yaba Wa Gwamnan Sokoto Kan Samar Wa Matasa Ayyukan Yi

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Adaidaita Sahu 650 Da Babura 1000 A Sokoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Larabar nan ne Gwamna Lawal na Jihar Zamfara ya jagoranci ƙaddamar da rabon wasu babura da A Daidaita Sahu da gwamnatin Jihar Sakoto ta samar.

Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa takwaransa na jihar Sokoto, Dr Ahmed Aliyu bisa ƙara samar da guraben ayyukan yi ga al’ummar jihar musamman matasa.

A ranar Larabar nan ne Gwamna Lawal ya jagoranci ƙaddamar da rabon wasu babura da A Daidaita Sahu da gwamnatin Jihar Sokoto ta samar.

Sokoto

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Sakkwato ta sayo A Daidaita Sahu 500, babura 1,000, da A Daidaita Sahu mai amfani da lantarki guda 150 domin raba wa matasa a faɗin jihar a matsayin wani mataki na ƙarfafa tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Har Yanzu Tana Biyan Kudin Tallafin Man Fetur 

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, a jawabin da ya gabatar yayin bikin ƙaddamarwar, Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa Gwamnan Jihar Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, bisa wannan gagarumin shiri. Ya ce, “Wannan shiri ne da ya dace, musamman idan aka yi la’akari da mawuyacin halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki sakamakon janye tallafin man fetur da taɓarɓarewar kasuwar canji, wanda ke haifar da hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar nan.

Sokoto

“Ina kira ga waɗanda suka ci gajiyar wannan shiri da su yi amfani da damar da aka ba su wajen dogaro da kai da tallafa wa iyalansu, da kuma bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin yankin.

“Adaidaita sahun da za a raba, masu amfani da wutar lantarki ne. Suna da muhimmanci idan aka yi la’akari a kan yanayin da duniya ke canjawa a hankali daga amfani da motocin da suka dogara da albarkatun mai. Motocin lantarki suna da kyau ga muhalli da tattalin arziki, idan aka yi la’akari da tashin farashin man fetur.

“Amfani da su a hanyar sufuri zai yi matuƙar tasiri wajen samar da guraben ayyukan yi ga matasa, wuraren cajin su da makanikan da za su samar da kayan gwaran su”

Gwamna Lawal ya ƙara tabbatar da cewa, gayyatar da aka yi masa a matsayin babban baƙo na nuni ne ga kyakykyawan alaƙar da ke tsakanin al’ummar Sakkwato da Zamfara, wanda hakan ke ƙara zamanantar da Nijeriya.

Sokoto

“Tare da tarihinmu, al’adunmu, da tsarin ci gaba, dole ne mu ci gaba da ba da goyon baya da ƙarfafa juna a kowane lokaci don inganta al’ummarmu. Za mu ci gaba da lalubo hanyoyin haɗin gwiwa don gina kyakkyawar makoma ga jihohinmu biyu.

“Da waɗannan kalamai, ina mai farin cikin sanar da jama’a cewa, domin ɗaukakar Allah Maɗaukakin Sarki da kuma amfanin bil’adama, na ƙaddamar da rabon da babura a matsayin ƙarfafa tattalin arziki ga matasa a faɗin Jihar Sakkwato.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adaidaita SahuBaburaKaddamarwaMatasaSokotoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Musanta Ci Gaba Da Biyan Tallafin Man Fetur

Next Post

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

Related

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

28 minutes ago
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

2 hours ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

3 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

11 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

12 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

14 hours ago
Next Post
An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari'a Kan Rikicin Masarautar Kano

LABARAI MASU NASABA

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.