ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Adaidaita Sahu 650 Da Babura 1000 A Sokoto

Ya Yaba Wa Gwamnan Sokoto Kan Samar Wa Matasa Ayyukan Yi

by Leadership Hausa
2 years ago
Sokoto

A ranar Larabar nan ne Gwamna Lawal na Jihar Zamfara ya jagoranci ƙaddamar da rabon wasu babura da A Daidaita Sahu da gwamnatin Jihar Sakoto ta samar.

Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa takwaransa na jihar Sokoto, Dr Ahmed Aliyu bisa ƙara samar da guraben ayyukan yi ga al’ummar jihar musamman matasa.

A ranar Larabar nan ne Gwamna Lawal ya jagoranci ƙaddamar da rabon wasu babura da A Daidaita Sahu da gwamnatin Jihar Sokoto ta samar.

ADVERTISEMENT

Sokoto

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Sakkwato ta sayo A Daidaita Sahu 500, babura 1,000, da A Daidaita Sahu mai amfani da lantarki guda 150 domin raba wa matasa a faɗin jihar a matsayin wani mataki na ƙarfafa tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Har Yanzu Tana Biyan Kudin Tallafin Man Fetur 

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, a jawabin da ya gabatar yayin bikin ƙaddamarwar, Gwamna Dauda Lawal ya yaba wa Gwamnan Jihar Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, bisa wannan gagarumin shiri. Ya ce, “Wannan shiri ne da ya dace, musamman idan aka yi la’akari da mawuyacin halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki sakamakon janye tallafin man fetur da taɓarɓarewar kasuwar canji, wanda ke haifar da hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar nan.

Sokoto

“Ina kira ga waɗanda suka ci gajiyar wannan shiri da su yi amfani da damar da aka ba su wajen dogaro da kai da tallafa wa iyalansu, da kuma bayar da gudunmawa ga tattalin arzikin yankin.

“Adaidaita sahun da za a raba, masu amfani da wutar lantarki ne. Suna da muhimmanci idan aka yi la’akari a kan yanayin da duniya ke canjawa a hankali daga amfani da motocin da suka dogara da albarkatun mai. Motocin lantarki suna da kyau ga muhalli da tattalin arziki, idan aka yi la’akari da tashin farashin man fetur.

“Amfani da su a hanyar sufuri zai yi matuƙar tasiri wajen samar da guraben ayyukan yi ga matasa, wuraren cajin su da makanikan da za su samar da kayan gwaran su”

Gwamna Lawal ya ƙara tabbatar da cewa, gayyatar da aka yi masa a matsayin babban baƙo na nuni ne ga kyakykyawan alaƙar da ke tsakanin al’ummar Sakkwato da Zamfara, wanda hakan ke ƙara zamanantar da Nijeriya.

Sokoto

“Tare da tarihinmu, al’adunmu, da tsarin ci gaba, dole ne mu ci gaba da ba da goyon baya da ƙarfafa juna a kowane lokaci don inganta al’ummarmu. Za mu ci gaba da lalubo hanyoyin haɗin gwiwa don gina kyakkyawar makoma ga jihohinmu biyu.

“Da waɗannan kalamai, ina mai farin cikin sanar da jama’a cewa, domin ɗaukakar Allah Maɗaukakin Sarki da kuma amfanin bil’adama, na ƙaddamar da rabon da babura a matsayin ƙarfafa tattalin arziki ga matasa a faɗin Jihar Sakkwato.”

Sokoto
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari’a Kan Rikicin Masarautar Kano

An Tsaurara Tsaro Bayan Fara Shari'a Kan Rikicin Masarautar Kano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.