• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Aikin Titi A Jihar Ribas

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Aikin Titi A Jihar Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yaba wa ƙoƙarin Gwamna Siminalayi Fubara kan ayyukan raya ƙasa daban-daban a Jihar Ribas.

 

Gwamna Lawal ya kasance babban baƙo na musamman a wajen ƙaddamar da aikin titin da gadojin Opobo, wanda ya gudana a ranar Litinin a ƙaramar hukumar Opobo/Nkoro.

  • Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Lashi Takobin Zamowar Kasar Sin Ginshikin Zaman Lafiya Da Hadaka

Da yake gabatar da jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa kammala aikin titin Opobo da gadoji ya nuna yadda Fubara ke da himma wajen bunƙasa ababen more rayuwa da inganta zamantakewa da tattalin arziki da jin daɗin al’ummar jihar Ribas.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Ci gaban ababen more rayuwa, kamar yadda muka sani, wani ginshiƙi ne na ci gaban tattalin arziki da ci gaban al’umma. Hanyar Opobo da tare da gada babu shakka za ta ƙara samar da haɗin kai, inganta kasuwanci, da sauƙaƙe samun dama ga muhimman ayyuka ga mazauna Opobo da kewaye.

 

“Samar da ingantattun hanyoyin sufuri zai haifar da ayyukan tattalin arziki da kuma buɗe sabbin damarmaki ga al’ummomi a ciki da wajen jihar. Ingantattun ababen more rayuwa tabbas za su jawo hannun jari, da bunƙasa yawon buɗe ido, da ɗaga darajar al’ummar Opobo a idon duniya”

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da nanata cewa Gwamna Fubara ya jajirce wajen ganin gwamnatinsa ta kawo sauyi ga ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a jihar Zamfara.

 

“Muna da ra’ayi ɗaya cewa ingantattun ababen more rayuwa su ne ginshiƙi wajen raya ayyukan tattalin arziki da kuma ɗaukaka matsayin rayuwar jama’armu. A Zamfara, muna samun ci gaba mai ban mamaki ta hanyar ginawa da kuma gyara wasu muhimman ayyuka a faɗin jihar.

 

“Filin jirgin sama na Gusau da ke gudana, da kuma gina babbar hanyar sadarwa ta karkara da birane, shaida ne ƙarara kan burinmu na ingantawa da kuma zamanantar da muhimman ababen more rayuwa don inganta rayuwar al’ummarmu. Waɗannan ayyukan sun daidaita tare da hangen nesa namu don ƙirƙirar dama da kafa tushe mai ƙarfi don samun ci gaba mai ɗorewa.

 

“Ina yaba wa Gwamna Fubara bisa jajircewarsa na ci gaban jihar Ribas. Wannan sadaukarwar da ya yi don samar da makoma mai kyau ga jama’arsa abu ne mai ban sha’awa da gaske kuma abin koyi ne ga sauran jihohi.

 

“Har ila yau, ina gode masa saboda karramawar da aka yi min na kasancewa cikin wannan gagarumin taron. Ina da yaƙinin cewa hanyar Opobo da gadoji za su kawo wa al’ummar Opobo alfanu mai ɗorewa tare da ba da gudummawa sosai ga ci gaban jihar Ribas baki ɗaya.”

 

Tun da farko Gwamna Siminalayi Fubara ya nuna jin dafinsa ga Gwamna Lawal bisa amsa gayyatar da aka yi masa na zama babban baƙo.

 

Gwamna Fubara ya bayyana cewa gwamnatin da ta gabata ta ƙaddamar da aikin gina titin zobe na Opobo da gadoji a ranar 28 ga Mayu, 2023. “Mun ɗauki nauyin sake fasalin aikin tare da ɗaukaka shi zuwa matsayin da yake a yanzu. Wannan aikin yana da muhimmanci a gare ni, kuma na yi farin cikin ƙaddamar da shi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Ci Gaba Da Goya Wa PCACC Baya Wajen Yaƙar Cin Hanci Da Rashawa – Gwamnatin Kano

Next Post

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

27 minutes ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

2 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

3 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

7 hours ago
Zamfara
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

8 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

9 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.