ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Aikin Titi A Jihar Ribas

by Sulaiman
1 year ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yaba wa ƙoƙarin Gwamna Siminalayi Fubara kan ayyukan raya ƙasa daban-daban a Jihar Ribas.

 

Gwamna Lawal ya kasance babban baƙo na musamman a wajen ƙaddamar da aikin titin da gadojin Opobo, wanda ya gudana a ranar Litinin a ƙaramar hukumar Opobo/Nkoro.

ADVERTISEMENT
  • Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Lashi Takobin Zamowar Kasar Sin Ginshikin Zaman Lafiya Da Hadaka

Da yake gabatar da jawabinsa a wajen ƙaddamar da aikin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa kammala aikin titin Opobo da gadoji ya nuna yadda Fubara ke da himma wajen bunƙasa ababen more rayuwa da inganta zamantakewa da tattalin arziki da jin daɗin al’ummar jihar Ribas.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“Ci gaban ababen more rayuwa, kamar yadda muka sani, wani ginshiƙi ne na ci gaban tattalin arziki da ci gaban al’umma. Hanyar Opobo da tare da gada babu shakka za ta ƙara samar da haɗin kai, inganta kasuwanci, da sauƙaƙe samun dama ga muhimman ayyuka ga mazauna Opobo da kewaye.

 

“Samar da ingantattun hanyoyin sufuri zai haifar da ayyukan tattalin arziki da kuma buɗe sabbin damarmaki ga al’ummomi a ciki da wajen jihar. Ingantattun ababen more rayuwa tabbas za su jawo hannun jari, da bunƙasa yawon buɗe ido, da ɗaga darajar al’ummar Opobo a idon duniya”

 

Gwamna Lawal ya ci gaba da nanata cewa Gwamna Fubara ya jajirce wajen ganin gwamnatinsa ta kawo sauyi ga ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a jihar Zamfara.

 

“Muna da ra’ayi ɗaya cewa ingantattun ababen more rayuwa su ne ginshiƙi wajen raya ayyukan tattalin arziki da kuma ɗaukaka matsayin rayuwar jama’armu. A Zamfara, muna samun ci gaba mai ban mamaki ta hanyar ginawa da kuma gyara wasu muhimman ayyuka a faɗin jihar.

 

“Filin jirgin sama na Gusau da ke gudana, da kuma gina babbar hanyar sadarwa ta karkara da birane, shaida ne ƙarara kan burinmu na ingantawa da kuma zamanantar da muhimman ababen more rayuwa don inganta rayuwar al’ummarmu. Waɗannan ayyukan sun daidaita tare da hangen nesa namu don ƙirƙirar dama da kafa tushe mai ƙarfi don samun ci gaba mai ɗorewa.

 

“Ina yaba wa Gwamna Fubara bisa jajircewarsa na ci gaban jihar Ribas. Wannan sadaukarwar da ya yi don samar da makoma mai kyau ga jama’arsa abu ne mai ban sha’awa da gaske kuma abin koyi ne ga sauran jihohi.

 

“Har ila yau, ina gode masa saboda karramawar da aka yi min na kasancewa cikin wannan gagarumin taron. Ina da yaƙinin cewa hanyar Opobo da gadoji za su kawo wa al’ummar Opobo alfanu mai ɗorewa tare da ba da gudummawa sosai ga ci gaban jihar Ribas baki ɗaya.”

 

Tun da farko Gwamna Siminalayi Fubara ya nuna jin dafinsa ga Gwamna Lawal bisa amsa gayyatar da aka yi masa na zama babban baƙo.

 

Gwamna Fubara ya bayyana cewa gwamnatin da ta gabata ta ƙaddamar da aikin gina titin zobe na Opobo da gadoji a ranar 28 ga Mayu, 2023. “Mun ɗauki nauyin sake fasalin aikin tare da ɗaukaka shi zuwa matsayin da yake a yanzu. Wannan aikin yana da muhimmanci a gare ni, kuma na yi farin cikin ƙaddamar da shi.”

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Za Ta Tsawaita Kasafin 2024 Zuwa Watanni 6 – Akpabio

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.