ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista

by Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da cewa shekarar 2025 za ta zama shekarar da za a ƙarfafa gyare-gyaren da ake aiwatarwa ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannonin tsarin tattalin arziki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin taron atisayen shugabanci da gudanarwa wanda gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya shirya wa ma’aikatan sa.

ADVERTISEMENT
  • Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Miƙo Mata Rabonta Na Tsawon Shekaru 25 Daga Shirin NLNG 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Lashi Takobin Zamowar Kasar Sin Ginshikin Zaman Lafiya Da Hadaka

A jawabin sa, Idris ya jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen bayyana nasarorin gwamnatin.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ya ce: “Babu tantama, ina tabbatar maku da cewa shekarar 2025 za ta ƙarfafa gyare-gyaren Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannoni daban-daban na rayuwar mu ta zamantakewa, tattalin arziki, da siyasa.”

 

Ministan ya jaddada shirin Shugaba Tinubu na aiwatar da manyan gyare-gyaren kuɗi don ƙara wa jihohi da ƙananan hukumomi yawan kuɗaɗen da suke samu domin ciyar da al’ummar Nijeriya gaba, bisa tsarin gaskiya na tarayya.

 

Ya yi kira ga VON, a matsayin sa na gidan watsa labaran ƙasa da ƙasa, da ya bayyana wa da duniya nasarorin da Nijeriya take samu.

 

Ya ce, “Dole ne gidan rediyon Muryar Nijeriya ya sanar wa da duniya cewa Nijeriya ta dawo kan turbar aiki; cewa muna samun nasara a yaƙin da muke yi da ta’addanci, ’yan fashi, da rikicin ƙabilanci; cewa muna ƙarfafa al’ummar mu domin samar da cigaba mai ɗorewa; cewa matasan mu sun samu hanya mafi sauƙi don ilimi mai inganci ta hanyar Asusun Ba da Lamuni na Ilimi na Ƙasa (NEL), sannan kuma abu mafi muhimmanci, cewa ƙasar mu tana kan matakin sauyin makamashi wanda zai tabbatar da wutar lantarki da iskar gas mai ɗorewa don amfani a gidaje da masana’antu.”

 

Ya ƙara da cewa dole ne VON ta tabbatar “ba a bar giɓi ba wajen tattara nasarorin da Nijeriya take samu” ta hanyar rahotanni da nazari da ake watsa wa al’ummar duniya.

 

Idris ya nanata cewa gwamnati za ta ci gaba da amfani da damar da VON take da ita domin yaƙar barazanar labaran ƙarya waɗanda ke barazana ga ƙasar nan a matakin duniya.

 

Ministan ya yi kira ga ƙungiyoyin kafofin watsa labarai kamar VON da su rungumi fasahohin zamani domin su ci gaba da yin gogayya a duniyar watsa labarai, tare da inganta inganci da isar da shirye-shiryen su.

 

Ya kuma yaba wa Darakta-Janar na VON, Malam Jibrin Baba Ndace, tare da masu gudanarwa da ma’aikatan VON bisa sadaukarwar su da hangen nesa wajen tafiyar da hukumar zuwa ga kyakkyawan aiki.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
NBS

'Yan Nijeriya Sun Biya Kudin Fansa Naira Tiriliyan 2.23 Ga Masu Garkuwa Da Mutane A Cikin watanni 12 – NBS

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.