ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da cewa shekarar 2025 za ta zama shekarar da za a ƙarfafa gyare-gyaren da ake aiwatarwa ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannonin tsarin tattalin arziki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin taron atisayen shugabanci da gudanarwa wanda gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) ya shirya wa ma’aikatan sa.

ADVERTISEMENT
  • Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Miƙo Mata Rabonta Na Tsawon Shekaru 25 Daga Shirin NLNG 
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Lashi Takobin Zamowar Kasar Sin Ginshikin Zaman Lafiya Da Hadaka

A jawabin sa, Idris ya jaddada rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen bayyana nasarorin gwamnatin.

 

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ya ce: “Babu tantama, ina tabbatar maku da cewa shekarar 2025 za ta ƙarfafa gyare-gyaren Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa, waɗanda tuni suke haifar da sakamako mai kyau a fannoni daban-daban na rayuwar mu ta zamantakewa, tattalin arziki, da siyasa.”

 

Ministan ya jaddada shirin Shugaba Tinubu na aiwatar da manyan gyare-gyaren kuɗi don ƙara wa jihohi da ƙananan hukumomi yawan kuɗaɗen da suke samu domin ciyar da al’ummar Nijeriya gaba, bisa tsarin gaskiya na tarayya.

 

Ya yi kira ga VON, a matsayin sa na gidan watsa labaran ƙasa da ƙasa, da ya bayyana wa da duniya nasarorin da Nijeriya take samu.

 

Ya ce, “Dole ne gidan rediyon Muryar Nijeriya ya sanar wa da duniya cewa Nijeriya ta dawo kan turbar aiki; cewa muna samun nasara a yaƙin da muke yi da ta’addanci, ’yan fashi, da rikicin ƙabilanci; cewa muna ƙarfafa al’ummar mu domin samar da cigaba mai ɗorewa; cewa matasan mu sun samu hanya mafi sauƙi don ilimi mai inganci ta hanyar Asusun Ba da Lamuni na Ilimi na Ƙasa (NEL), sannan kuma abu mafi muhimmanci, cewa ƙasar mu tana kan matakin sauyin makamashi wanda zai tabbatar da wutar lantarki da iskar gas mai ɗorewa don amfani a gidaje da masana’antu.”

 

Ya ƙara da cewa dole ne VON ta tabbatar “ba a bar giɓi ba wajen tattara nasarorin da Nijeriya take samu” ta hanyar rahotanni da nazari da ake watsa wa al’ummar duniya.

 

Idris ya nanata cewa gwamnati za ta ci gaba da amfani da damar da VON take da ita domin yaƙar barazanar labaran ƙarya waɗanda ke barazana ga ƙasar nan a matakin duniya.

 

Ministan ya yi kira ga ƙungiyoyin kafofin watsa labarai kamar VON da su rungumi fasahohin zamani domin su ci gaba da yin gogayya a duniyar watsa labarai, tare da inganta inganci da isar da shirye-shiryen su.

 

Ya kuma yaba wa Darakta-Janar na VON, Malam Jibrin Baba Ndace, tare da masu gudanarwa da ma’aikatan VON bisa sadaukarwar su da hangen nesa wajen tafiyar da hukumar zuwa ga kyakkyawan aiki.

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
NBS

'Yan Nijeriya Sun Biya Kudin Fansa Naira Tiriliyan 2.23 Ga Masu Garkuwa Da Mutane A Cikin watanni 12 – NBS

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.