• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
3 hours ago
Dabbobi

Gwanatin tarayya ta dauki matakin gaggawa na dakile yaduwar barkewar kwayoyin cutar kama kafafu da bakin dabbobi da ta bulla a wata gona da ake kiwon dabbobi a Birnin Kudu na Jihar Jigawa.

Ma’aikatar kula da bunkasa kiwon dabbobi ta tarayya, ta bayyana haka ne a cikin sanawar da ta fitar.

  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sanarwar ta ce, ma’aiktar ta tura tawagar kwararrun likitoci takwas a karkashin jagorancin, Dakta Adeniyi Adedoyin, Darakta a sashen tsara ayyuka a ma’aikatar zuwa gonar ta kiwon dabbobin da ke Birnin Kudu, domin dakile yaduwar kwayoyin cutar.

Daga cikin tawagar, akwai kuma wasu kwararru daga cibiyar gudanar da binciken kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI) da wasu daga ma’aikatar ta kula da bunkasa kiwon dabbobi tare da taimakawar jami’an da ke kula da lafiya dabbobi ta Jigawa da kuma wasu shugabanni daga bangaren Kungiyar Fulani Makiyaya ta Miyetti Allah.

Tawagar a gonar ta Mallam Alu Agro-Allied da annobar ta bulla, sun gano cewa; kimanin dabbobi 34 ne dauke da alamomin cutar, inda kuma tuni dabbobi shida da cutar ta harba, suka mutu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Kazalika, tawagar ta kuma dauki alamomin kwayar cutar; domin yin gwajin tare kuma da kaddamar da yin Allurar rigafi ga dabbobin da ake kiwo da ke daura da gonar.

“Wannan matakin da aka dauka na gaggawa, ya nuna yadda ma’aikatar ta mayar da hankali, wajen tabbatar da kare lafiyar dabbobi, duba da cewa; fannin ne da ke kara taimakawa, wajen kara habaka tattalin arzikin kasar,” in ji Adedoyin.

“Ta hanyar aikin hadaka da muke ci gaba da gudanawa, muna kare hanyoyin sana’ar masu yin kiwon ne da kuma kara taimaka wa shirin shugaban kasa na sake farfado da fata, wato na ‘Renewed Hope Agenda’ tare kuma da shirin dabarun bunkasa kiwo na kasa (NLGAS),” a cewar Adedoyin.

Shi kuwa, Jami’i a Cibiyar Gudanar da Binciken Kula da Lafiyar Dabbobi ta Kasa (NBRI) Hussain Ularamu, ya jaddada bukatar a rika kai rahoton bullar duk wata kwayar cuta ga hukumomin da suka kamata tare kuma da adana bayanan kwayoyin cutar, domin daukar matakan gaggawa.

Kazalika, a lokacin kai daukin, ma’aikatar ta wayar da kan Fulani Makiyaya da wasu masu kiwo, kan muhimmancin tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon dabbobinsu da kuma lokutan da ya kamata a rika yi wa dabbobin allurra rigakafi.

Su ma, a jawabansu daban-daban, Manajan Kula da Gonar Isa Mohammed Gadama da kuma Shugaban Kungiyar Miyetti Allah reshen jihar, Adamu Kankau, sun yaba wa gwamnatin tarayya kan daukin gaggawar da ta kawo a gonar, inda suka yi alkawarin ci gaba da bayar da hadin kai.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ma’aiktar Bunkasa Kiwon Dabbobi na Jihar Jigawa, Salem Abdurrahman, ya sanar da cewa; ma’aikatarsa, ta himmatu wajen gudanar da yi wa dabbobi allurar rigakafi a duk shekara tare kuma da ci gaba da sanya ido, kan bullar duk wata kwayar cuta da ke harbin dabbobi a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
Manyan Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
Manyan Labarai

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Next Post
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.