• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
8 months ago
in Al'ajabi
0
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Makarantar Ittihadil Ummah Alal-Sunnati Muhammadin (SAW) ta Unguwar Hausawa Garin Jiwa dake Abuja, ta gabatar da walimar saukar karatun Alkur’ani mai Girma, inda ta yaye dalibai guda takwai dukkansu dattawa.

Wani abin mamaki da ba a saba gani ba shi ne, a bisa al’ada yara da matasa aka sani ana yi wa iri wannan walima ta saukar karatu, sai ga shi yau kuma wannan makaranta ta yaye magidanta mata masu shekaru dattaku., Wadannan dalibai sun fara ne tun daga babbaku har zuwa fara koyon rubutu, suka kai ga sun rubuta Kur’ani yadda ake yinsa a allo har kuma suka dawo Tajwid suka samu gogewa akan hakan suka samu damar rubutawa karantawa da kuma samun haddar wasu izu daga Alkur’ani da a halin yanzu dai sun dauki aniyar haddar Kur’ani tun daga Bakara zuwa Nasi.

  • Manyan Jigajigan ‘Yan Jam’iyyun Adawa Da Suka Sauya Sheka Zuwa APC A 2024
  • Tattaunawar Wakilin CMG Da Ministan Harkokin Wajen Iran

Wakilinmu ya samu zantawa da shugaban makarantar Ustaz Yahaya Balarabe Abdullahi Pandogari, ya bayyana nasarar da suka samu a matsayin jajircewarsu da kuma samun hadin kan wadannan dalibai dattawa. Ya nuna muhimmancin ilimi ga dattawa musamman na Alkur’ani a wannan zamani da wasu ke ganin ilimi ne kawai na yara da matasa musamman idan shekaru sun cin musu.

A karshe ya yi kira da shugabanni su ji tsoron Allah cikin amanar jagorancin da Allah ya wakilta su.

Daliban sun taka muhimmar rawa wajen karanta Kur’ani yadda ya kamata tare da ba wa kowane baki hakkinsa, baya ga amsa tambayoyi a fannin Tajwid. Daliban da suka samu nasarar kammala wannan karatu gami da karbar allo mai dauke da zayyana takardar shaida, sun hada da Alhaji Isa Usman, Muhammad Sani Umar, Alhaji Haruna Ibrahim Malam Isa Auwal, Alhaji Yahaya Garba, Malam Zubairu Adamu, da Alhaji Ashafa Khamis.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Wannan makaranta ta Madarastul Ittihadil Ummah tana rassa a Jihohin Kano, Jos a Filato da sauran jihohi inda ta samu nasarar yaye irin wadannan dalibai masu shekaru daga 50 zuwa sama masana kuma mahadda Kur’ani.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Jigajigan ‘Yan Jam’iyyun Adawa Da Suka Sauya Sheka Zuwa APC A 2024

Next Post

Dalilin Da Ya Sa Legas, Abuja, Kaduna Suka Samu Masu Zuba Hannun Jari A Zango Na Uku

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

2 months ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

2 months ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

3 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

4 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

4 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

4 months ago
Next Post
Dalilin Da Ya Sa Legas, Abuja, Kaduna Suka Samu Masu Zuba Hannun Jari A Zango Na Uku

Dalilin Da Ya Sa Legas, Abuja, Kaduna Suka Samu Masu Zuba Hannun Jari A Zango Na Uku

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.