• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi

by Rabi'u Ali Indabawa
4 months ago
in Kasashen Ketare
0
Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

Yoon Suk Yeol ya zamo shugaban kasa na farko mai ci da aka taba tsarewa a Koriya ta Kudu bayan da jami’ai masu bincike suka kawar da shinge da karya wayar da ta kange gidan domin su kamo shi.

Ana binciken Yoon mai shekaru 64 ne dai bisa tuhumar tayar da tarzoma a kasar bayan da ya gaza sauya dokokin kasar da na tsarin mulkin soja a watan Disambar 2024 wani abu da ya jefa kasar cikin rudani.

  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano
  • Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Da ma dai majalisar dokokin kasar ta riga ta tsige mr Yoon daga kujerar shugaban kasar to sai dai za a iya tunbuke shi daga kan kujerar ne kawai idan kotun tsarin mulkin kasar ta amince da tsigewar.

To amma tsare mista Yoon din na ranar Laraba ya kawo karshen makonni biyu da aka kwashe ana zaman tankiya tsakanin masu binciken da masu tsaron lafiyar shugaban kasa.

Masu binciken dai daga sashen binciken laifukan rashawa da cin hanci sun gaza kama shugaban kasar a ranar 3 ga watan Janairu sakamakon kwashe awanni shida suna tataburza da dakarun shugaban kasar.

Da asubar ranar Laraba ne kuma tawagar masu binciken ta samu dauki ta hanyar kara yawansu inda suka kai mutum dubu daya tare da ‘yansanda suka yi dirar mikiya a gidan shugaban kasar da ke tsakiyar birnin Seol, inda suka yi amfani da tsanuka wajen hawa katangar gidan da wasu manyan motoci da suka yi musu shinge daga tarar da shugaban.

Kuma bayan kwashe awanni, sai hukumomi suka sanar da cewa an kama mista Yoon.

A wani bidiyo mai tsawon minti uku da aka wallafa, mista Yoon ya ce zai bayar da hadin kai dangane da binciken da ake yi masa duk da dai ya ce kama shi da binciken da ake yi masa ba halattattu ba ne.

Lauyoyin mista Yoon sun ce tsarewar ta saba dokokin kasar. To sai dai kotun kolin kasar ta ce tsarewar an yi ne bisa doka.

A yanzu haka dai ministan kudin kasar, Choi Sang-mok ne ke rikon kwaryar jagorancin kasar sakamakon tsige mataimakin shugaban kasar na farko, Han Duck-soo da majalisar dokokin kasar – da ‘yan hamayya suke da rinjaye, ta yi

Wace dama Yoon ke da ita?

Bisa tsarin sammaci, masu binciken ka iya rike mista Yoon har tsawon awanni 48, kuma daga nan ne suke bukatar samun sabon sammaci na ci gaba da tsare shi domin ci gaba da bincike.

Idan aka samu wannan sammaci, to za su iya ci gaba da tsare shi har tsawon karin kwana 20 kafin a gurfanar da shi a gaban kuliya.

Idan kuma ba a samu sabon sammacin ba to dole ne a sake shi bayan karewar awanni 48 din.

Magoya bayan mista Yoon dai na ci gaba da gudanar da zanga-zanga domin nuna kin amincewarsu da kamun nasa.

Sun yi dandazo a gaban gidansa tun kafin asubahin ranar Laraba, inda suka kasance daura da masu hamayya da shi.

Waiwaye

Kasar Koriya ta Kudu dai ta yi fama da matsalolin siyasa tun bayan da sanar da sauya dokar kasar da ta mulkin sojoji a ranar 3 ga watan Disamban 2024 wanda ya janyo ‘yan majalsiar dokoki suka tsallaka katanga yayin shiga majalisa domin kin amincewa da dokar.

Shugaban ya ce yana kare kasar ne daga wasu mutane da ke kishiyantar kasar da ke goyon bayan Koriya ta Arewa, amma kuma ba jimawa sai ta bayyana cewa burinsa na siyasa ne ya haifar da hakan.

Shi dai Mista Yoon ya kasance shugaban kasan da ba shi da katabus tun bayan da ‘yan hamayya suka lashe babban zaben kasar da aka yi a watan Afrilu da gagarumar nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamawaKoriyaShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Neman Tsige Sarkin Zazzau

Next Post

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

4 hours ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

1 day ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

6 days ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.