• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi

by Rabi'u Ali Indabawa
8 months ago
in Kasashen Ketare
0
Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

Yoon Suk Yeol ya zamo shugaban kasa na farko mai ci da aka taba tsarewa a Koriya ta Kudu bayan da jami’ai masu bincike suka kawar da shinge da karya wayar da ta kange gidan domin su kamo shi.

Ana binciken Yoon mai shekaru 64 ne dai bisa tuhumar tayar da tarzoma a kasar bayan da ya gaza sauya dokokin kasar da na tsarin mulkin soja a watan Disambar 2024 wani abu da ya jefa kasar cikin rudani.

  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano
  • Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Da ma dai majalisar dokokin kasar ta riga ta tsige mr Yoon daga kujerar shugaban kasar to sai dai za a iya tunbuke shi daga kan kujerar ne kawai idan kotun tsarin mulkin kasar ta amince da tsigewar.

To amma tsare mista Yoon din na ranar Laraba ya kawo karshen makonni biyu da aka kwashe ana zaman tankiya tsakanin masu binciken da masu tsaron lafiyar shugaban kasa.

Masu binciken dai daga sashen binciken laifukan rashawa da cin hanci sun gaza kama shugaban kasar a ranar 3 ga watan Janairu sakamakon kwashe awanni shida suna tataburza da dakarun shugaban kasar.

Da asubar ranar Laraba ne kuma tawagar masu binciken ta samu dauki ta hanyar kara yawansu inda suka kai mutum dubu daya tare da ‘yansanda suka yi dirar mikiya a gidan shugaban kasar da ke tsakiyar birnin Seol, inda suka yi amfani da tsanuka wajen hawa katangar gidan da wasu manyan motoci da suka yi musu shinge daga tarar da shugaban.

Kuma bayan kwashe awanni, sai hukumomi suka sanar da cewa an kama mista Yoon.

A wani bidiyo mai tsawon minti uku da aka wallafa, mista Yoon ya ce zai bayar da hadin kai dangane da binciken da ake yi masa duk da dai ya ce kama shi da binciken da ake yi masa ba halattattu ba ne.

Lauyoyin mista Yoon sun ce tsarewar ta saba dokokin kasar. To sai dai kotun kolin kasar ta ce tsarewar an yi ne bisa doka.

A yanzu haka dai ministan kudin kasar, Choi Sang-mok ne ke rikon kwaryar jagorancin kasar sakamakon tsige mataimakin shugaban kasar na farko, Han Duck-soo da majalisar dokokin kasar – da ‘yan hamayya suke da rinjaye, ta yi

Wace dama Yoon ke da ita?

Bisa tsarin sammaci, masu binciken ka iya rike mista Yoon har tsawon awanni 48, kuma daga nan ne suke bukatar samun sabon sammaci na ci gaba da tsare shi domin ci gaba da bincike.

Idan aka samu wannan sammaci, to za su iya ci gaba da tsare shi har tsawon karin kwana 20 kafin a gurfanar da shi a gaban kuliya.

Idan kuma ba a samu sabon sammacin ba to dole ne a sake shi bayan karewar awanni 48 din.

Magoya bayan mista Yoon dai na ci gaba da gudanar da zanga-zanga domin nuna kin amincewarsu da kamun nasa.

Sun yi dandazo a gaban gidansa tun kafin asubahin ranar Laraba, inda suka kasance daura da masu hamayya da shi.

Waiwaye

Kasar Koriya ta Kudu dai ta yi fama da matsalolin siyasa tun bayan da sanar da sauya dokar kasar da ta mulkin sojoji a ranar 3 ga watan Disamban 2024 wanda ya janyo ‘yan majalsiar dokoki suka tsallaka katanga yayin shiga majalisa domin kin amincewa da dokar.

Shugaban ya ce yana kare kasar ne daga wasu mutane da ke kishiyantar kasar da ke goyon bayan Koriya ta Arewa, amma kuma ba jimawa sai ta bayyana cewa burinsa na siyasa ne ya haifar da hakan.

Shi dai Mista Yoon ya kasance shugaban kasan da ba shi da katabus tun bayan da ‘yan hamayya suka lashe babban zaben kasar da aka yi a watan Afrilu da gagarumar nasara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamawaKoriyaShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Ayyana Ranar Yanke Hukunci Kan Neman Tsige Sarkin Zazzau

Next Post

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

6 days ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

2 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

2 weeks ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

3 weeks ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

3 weeks ago
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda
Kasashen Ketare

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

3 weeks ago
Next Post
Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.