• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jami’an Tsaro Suka Shiga Gidan Shugaban Kasar Koriya Ta Kudu Suka Kamo Shi

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Koriya

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Yoon Suk Yeol ya zamo shugaban kasa na farko mai ci da aka taba tsarewa a Koriya ta Kudu bayan da jami’ai masu bincike suka kawar da shinge da karya wayar da ta kange gidan domin su kamo shi.

Ana binciken Yoon mai shekaru 64 ne dai bisa tuhumar tayar da tarzoma a kasar bayan da ya gaza sauya dokokin kasar da na tsarin mulkin soja a watan Disambar 2024 wani abu da ya jefa kasar cikin rudani.

  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano
  • Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

Da ma dai majalisar dokokin kasar ta riga ta tsige mr Yoon daga kujerar shugaban kasar to sai dai za a iya tunbuke shi daga kan kujerar ne kawai idan kotun tsarin mulkin kasar ta amince da tsigewar.

To amma tsare mista Yoon din na ranar Laraba ya kawo karshen makonni biyu da aka kwashe ana zaman tankiya tsakanin masu binciken da masu tsaron lafiyar shugaban kasa.

Masu binciken dai daga sashen binciken laifukan rashawa da cin hanci sun gaza kama shugaban kasar a ranar 3 ga watan Janairu sakamakon kwashe awanni shida suna tataburza da dakarun shugaban kasar.

Da asubar ranar Laraba ne kuma tawagar masu binciken ta samu dauki ta hanyar kara yawansu inda suka kai mutum dubu daya tare da ‘yansanda suka yi dirar mikiya a gidan shugaban kasar da ke tsakiyar birnin Seol, inda suka yi amfani da tsanuka wajen hawa katangar gidan da wasu manyan motoci da suka yi musu shinge daga tarar da shugaban.

Kuma bayan kwashe awanni, sai hukumomi suka sanar da cewa an kama mista Yoon.

A wani bidiyo mai tsawon minti uku da aka wallafa, mista Yoon ya ce zai bayar da hadin kai dangane da binciken da ake yi masa duk da dai ya ce kama shi da binciken da ake yi masa ba halattattu ba ne.

Lauyoyin mista Yoon sun ce tsarewar ta saba dokokin kasar. To sai dai kotun kolin kasar ta ce tsarewar an yi ne bisa doka.

A yanzu haka dai ministan kudin kasar, Choi Sang-mok ne ke rikon kwaryar jagorancin kasar sakamakon tsige mataimakin shugaban kasar na farko, Han Duck-soo da majalisar dokokin kasar – da ‘yan hamayya suke da rinjaye, ta yi

Wace dama Yoon ke da ita?

Bisa tsarin sammaci, masu binciken ka iya rike mista Yoon har tsawon awanni 48, kuma daga nan ne suke bukatar samun sabon sammaci na ci gaba da tsare shi domin ci gaba da bincike.

Idan aka samu wannan sammaci, to za su iya ci gaba da tsare shi har tsawon karin kwana 20 kafin a gurfanar da shi a gaban kuliya.

Idan kuma ba a samu sabon sammacin ba to dole ne a sake shi bayan karewar awanni 48 din.

Magoya bayan mista Yoon dai na ci gaba da gudanar da zanga-zanga domin nuna kin amincewarsu da kamun nasa.

Sun yi dandazo a gaban gidansa tun kafin asubahin ranar Laraba, inda suka kasance daura da masu hamayya da shi.

Waiwaye

Kasar Koriya ta Kudu dai ta yi fama da matsalolin siyasa tun bayan da sanar da sauya dokar kasar da ta mulkin sojoji a ranar 3 ga watan Disamban 2024 wanda ya janyo ‘yan majalsiar dokoki suka tsallaka katanga yayin shiga majalisa domin kin amincewa da dokar.

Shugaban ya ce yana kare kasar ne daga wasu mutane da ke kishiyantar kasar da ke goyon bayan Koriya ta Arewa, amma kuma ba jimawa sai ta bayyana cewa burinsa na siyasa ne ya haifar da hakan.

Shi dai Mista Yoon ya kasance shugaban kasan da ba shi da katabus tun bayan da ‘yan hamayya suka lashe babban zaben kasar da aka yi a watan Afrilu da gagarumar nasara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga
Kasashen Ketare

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Next Post
Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.