ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

by Abubakar Abba
1 year ago
Jega

A ranar 9 ga watan Yulin 2024, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu; ya kaddamar da Kwamitin Fadar Shugaban Kasa, kan wanzar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi a Nijeriya.

Manufar ita ce, domin cimma burin farfado da fannin kiwo a fadin kasar baki-daya, wanda aka kiyasata samun akalla Naira tiriliyan 33, duba da yadda a fanin ke bayar da gudunmawa kasa da kashi uku cikin dari ga tattalin arzikin wannan kasa a duk shekara.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje

Kasancewar Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin guda cikin shugabanin kwamitin tare da wasu kwararrun mutane 23, Shugaban Kasa Tinubu kuma da kansa ne ke jagorantar kwamitin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, an kuma gindayawa kwamitin sharudda 16 na wanzar da sauye-sauye a fannin tare kuma da zamanantar da fannin na kiwo.

A rahoton farko, a bangaren rahoton Jega; ya bayar da wasu shawarwari, domin farfado da fannin; ciki har da kiwon don samun riba.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

A bangaren kiwon Kajin gidan gona, rahoton ya kiyasta tsintsayen da ake kiwo da suka kai kimanin miliyan 563, inda kwamtin ya shawarci gwamnatin tarayya da ta tallafa wa masu kiwon kajin gidan gonar su kimanin 185,000, da kayan aiki ga kanannan masu kiwon kajin gidan gona.

Kazalika, rahoton ya bayar da shawarar taimaka wa masu kiwon kaji kimanin 550,000; da sauran kungiyoyin da ke kiwon, wanda adadinsu ya kai 735,000.

Bugu da kari, rahoton ya kuma bayar da shawarar kula da saurin jinsin kajin cikin gidan da ake kiwatawa tare da samar da kayan aikin da ake adana naman da ake amfani da shi a cikin kasar.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kara habaka fannin kiwon kasar tare da kara karfafa kasuwancin fannin da suka hada da Cibiyar Bunkasa Binciken Kiwon Dabbobi da ke Garin Shika a Jihar Kaduna da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kirkiro da shirye-shiryen kiwon kajin gidan gona da samar da kayan zamani na gwajin lafiyar dabbobin tare kuma da samar da rijiyoyin burtsatsai da fitilu masu aiki da hasken rana a wuraren da masu kiwon kajin gidan gonan suke tare da samar da sassan kyankyasar kwan kajin gidan gona.

Kazakila, rahoton ya kuma bukaci a kara daga darajar kiwon kamar irin su Talo-talo, Agwagi, Tantabaru, Jimina da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, yin amfani da wadannan shawarwari, za su taimaka wajen kara samun masu zuba hannun jari a fannin na kiwo a kasar.

Har ila yau, rahoton ya kuma bayar da shawara tare da kirkiro da cibiyar gudanar da bincike kan kiwon kajin gidan gona, wacce za ta ksanace daya daga cikin sabbi guda takwas na cibiyoyin gudanar da bincike.

Kazalika, rahoton ya shawarci gwamnatin da ta kara daga darajar cibiyar gudanar da binciken kiwon dabbobi ta kasa (NAPRI) tare kuma da kara daga darajar cibiyar gudanar da bincike, kan kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI).

Jega
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Cafke Matashin Da Ya Yi Lalata 'Yar Makocinsa Mai Shekara Takwas

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.