ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rahoton Farfesa Jega Na Bukatar Taimaka Wa Masu Kiwon Kajin Gidan Gona

by Abubakar Abba
1 year ago
Jega

A ranar 9 ga watan Yulin 2024, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu; ya kaddamar da Kwamitin Fadar Shugaban Kasa, kan wanzar da sauye-sauye a fannin kiwon dabbobi a Nijeriya.

Manufar ita ce, domin cimma burin farfado da fannin kiwo a fadin kasar baki-daya, wanda aka kiyasata samun akalla Naira tiriliyan 33, duba da yadda a fanin ke bayar da gudunmawa kasa da kashi uku cikin dari ga tattalin arzikin wannan kasa a duk shekara.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje

Kasancewar Farfesa Attahiru Muhammadu Jega, a matsayin guda cikin shugabanin kwamitin tare da wasu kwararrun mutane 23, Shugaban Kasa Tinubu kuma da kansa ne ke jagorantar kwamitin.

ADVERTISEMENT

Kazalika, an kuma gindayawa kwamitin sharudda 16 na wanzar da sauye-sauye a fannin tare kuma da zamanantar da fannin na kiwo.

A rahoton farko, a bangaren rahoton Jega; ya bayar da wasu shawarwari, domin farfado da fannin; ciki har da kiwon don samun riba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

A bangaren kiwon Kajin gidan gona, rahoton ya kiyasta tsintsayen da ake kiwo da suka kai kimanin miliyan 563, inda kwamtin ya shawarci gwamnatin tarayya da ta tallafa wa masu kiwon kajin gidan gonar su kimanin 185,000, da kayan aiki ga kanannan masu kiwon kajin gidan gona.

Kazalika, rahoton ya bayar da shawarar taimaka wa masu kiwon kaji kimanin 550,000; da sauran kungiyoyin da ke kiwon, wanda adadinsu ya kai 735,000.

Bugu da kari, rahoton ya kuma bayar da shawarar kula da saurin jinsin kajin cikin gidan da ake kiwatawa tare da samar da kayan aikin da ake adana naman da ake amfani da shi a cikin kasar.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kara habaka fannin kiwon kasar tare da kara karfafa kasuwancin fannin da suka hada da Cibiyar Bunkasa Binciken Kiwon Dabbobi da ke Garin Shika a Jihar Kaduna da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma shawarci gwamnatin, ta kirkiro da shirye-shiryen kiwon kajin gidan gona da samar da kayan zamani na gwajin lafiyar dabbobin tare kuma da samar da rijiyoyin burtsatsai da fitilu masu aiki da hasken rana a wuraren da masu kiwon kajin gidan gonan suke tare da samar da sassan kyankyasar kwan kajin gidan gona.

Kazakila, rahoton ya kuma bukaci a kara daga darajar kiwon kamar irin su Talo-talo, Agwagi, Tantabaru, Jimina da sauran makamantansu.

Rahoton ya kuma yi nuni da cewa, yin amfani da wadannan shawarwari, za su taimaka wajen kara samun masu zuba hannun jari a fannin na kiwo a kasar.

Har ila yau, rahoton ya kuma bayar da shawara tare da kirkiro da cibiyar gudanar da bincike kan kiwon kajin gidan gona, wacce za ta ksanace daya daga cikin sabbi guda takwas na cibiyoyin gudanar da bincike.

Kazalika, rahoton ya shawarci gwamnatin da ta kara daga darajar cibiyar gudanar da binciken kiwon dabbobi ta kasa (NAPRI) tare kuma da kara daga darajar cibiyar gudanar da bincike, kan kula da lafiyar dabbobi ta kasa (NBRI).

Jega
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Cafke Matashin Da Ya Yi Lalata 'Yar Makocinsa Mai Shekara Takwas

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.