• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kamfanin Huawei Na Sin Ke Fadada Moriyar Fasahar Sadarwa A Tanzania

by CMG Hausa
3 years ago
Huawei

Sanin kowa ne cewa a zamanin yau, daya daga muhimman fannonin da ke ingiza ci gaban duniya shi ne fannin fasahar sadarwa, wanda karkashinsa, alummun duniya ke cin gajiyar musayar bayanai da sakwanni ta kafofi daban daban, ciki har da na wayar salula da yanar gizo ko intanet. Hakan ne ma ya sa a kasashe masu tasowa da dama, gwamnatoci ke kara azamar samar da manyan ababen more rayuwa a wannan fanni.

A yan shekarun baya bayan nan, kasar Sin na kara samun manyan nasarori a fannonin fasahar sadarwa ko ICT, matakin da ke kara ingiza ci gaban tattalin arziki da zamantakewar alummunta a dukkanin bangarori. Kuma kamfanonin kasar masu ruwa da tsaki suna kara taka rawar gani wajen fitar da fasahohinsu ga kasashen waje, ta yadda daukacin alummun duniya za su kai ga cin gajiya daga hakan.

  • China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya

Kamfanin Huawei mai gudanar da ayyukan raya fasahohin sadarwa na zamani na kasar Sin, daya ne daga manyan kamfanonin duniya da suka yi fice a wannan fage. Inda ko da a farkon makon nan ma ya sanya hannu kan wata yarjejeniyar fadada turakun samar da hidimar yanar gizo a kasar Tanzania.

Bayan kammalarsa, aikin wanda aka yi wa lakabi da NICTBB, zai samar da hidimar yanar gizo ga gundumomin kasar 23 dake kasar ta gabashin Afirka.

Tuni dai kamfanin na Huawei ya tabbatar da shirinsa na yin aiki tare da tsagin Tanzania, wajen ganin an cimma nasarar kafa manyan ababen more rayuwa da za su warware kalubalen da kasar ke fuskanta a fannin sadarwar yanar gizo, matakin da ko shakka babu zai bunkasa fannin fasahar sadarwa a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

A bangaren gwamnatin Tanzania kuwa, manufar wannan aiki na NICTBB shi ne hade dukkanin yankunan kasar da hidimar yanar gizo. Baya ga haka, aikin zai iya taimakawa Tanzania samun damar dunkulewa ta fuskar hidimar fasahar sadarwa da kasashe makwaftanta, kamar Zambia, da Malawi, da Kenya, da Uganda, da Rwanda, da Burundi.

Lura da wannan manufa, muna iya cewa kamfanin Huawei na kasar Sin na taka rawar gani wajen bunkasa fasahar sadarwa a kasashen Afirka, yayin da kasashen nahiyar ke fafutukar samun ci gaba a wannan muhimmin fanni, mai ba da damar bunkasa tattalin arziki da kyautata jin dadin bil adama. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma’a A Matsayin Ranar Sallah

Da Dumi-Dumi: Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma'a A Matsayin Ranar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025
Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025 Kamfanin GEIL

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ɗan Majalisa Na Shekarar 2025: Benjamin Okezie Kalu

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.