ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
China

Ofishin jakadancin China da ke Nijeriya ya musanta rahotannin da ke cewa yana daukar nauyin ayyukan ta’addanci a kasar a fakaice.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin ya wallafa a shafinsa na yanar gizo ya karyata rahoton da jaridar The Times of the UK ta wallafa, inda ta ce “Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice” a Nijeriya.

  • Xi Ya Aika Sakon Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafa Jami’ar Yunnan
  • Da Dumi-Dumi: An Ga Watan Shawwal A Saudiyya

China ta ce rahoton ya samo asali ne daga bayanan da ba a tantance ba da kuma wadanda ba a tabbatar da su ba.

ADVERTISEMENT

“Gwamnatin kasar Sin, da ofishin jakadancin kasar Sin da ke Nijeriya, a ko dabyaushe, suna karfafawa tare da yin kira ga kamfanoni da ‘yan kasar Sin da ke Nijeriya, da su kiyaye dokoki da ka’idojin Nijeriya, tare da aiwatar da dokokin gida da jagororin aiki, da muhalli, da lafiya da aminci, da sauransu, kuma za su ci gaba da kokarinsu a wannan fanni.

“Gwamnatin kasar Sin ta kasance kuma ba za ta taba shiga cikin kowane nau’i na taimakon ta’addanci ba.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

“Zarge-zargen da ke kunshe a cikin rahoton ba su da tushe balle makama, kuma rashin da’a ne, kuma an yi la’akari da manufar rahoton.

“A cikin shekaru da dama da suka gabata, hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen Sin da Nijeriya ya kawo fa’ida ta gaske ga alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kyautata jin dadin jama’ar kasashen biyu.

“Za mu ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Nijeriya don inganta ci gaba da magance matsalolin tsaro, muna maraba da abokan huldar kasa da kasa da su shiga kokarinmu da gaskiya, amma za mu yi watsi da duk wani shiri ko matakin da zai bata mana hadin gwiwa,” in ji ofishin jakadancin a cikin sanarwar.

Rahoton a cikin The Times da aka buga a ranar 15 ga Afrilu, 2023 ya yi ikirarin cewa Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice a Nijeriya don ruguza mafi girman tattalin arziki a Afirka.

A cewar rahoton, shugabannin ma’adinai na kasar Sin suna ba da tallafin kungiyoyin ‘yan ta’addan Nijeriya domin samun damar shiga ma’adinan kasar.

“Kamfanonin China da ke aiki a wasu sassan Nijeriya inda ake yawan kai hare-hare na kulla huldar tsaro da masu tada kayar baya…, in ji wani bangare na rahoton.

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.