ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

China Ta Musanta Daukar Nauyin Ta’addanci A Nijeriya

by Sadiq
3 years ago
China

Ofishin jakadancin China da ke Nijeriya ya musanta rahotannin da ke cewa yana daukar nauyin ayyukan ta’addanci a kasar a fakaice.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin ya wallafa a shafinsa na yanar gizo ya karyata rahoton da jaridar The Times of the UK ta wallafa, inda ta ce “Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice” a Nijeriya.

  • Xi Ya Aika Sakon Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafa Jami’ar Yunnan
  • Da Dumi-Dumi: An Ga Watan Shawwal A Saudiyya

China ta ce rahoton ya samo asali ne daga bayanan da ba a tantance ba da kuma wadanda ba a tabbatar da su ba.

ADVERTISEMENT

“Gwamnatin kasar Sin, da ofishin jakadancin kasar Sin da ke Nijeriya, a ko dabyaushe, suna karfafawa tare da yin kira ga kamfanoni da ‘yan kasar Sin da ke Nijeriya, da su kiyaye dokoki da ka’idojin Nijeriya, tare da aiwatar da dokokin gida da jagororin aiki, da muhalli, da lafiya da aminci, da sauransu, kuma za su ci gaba da kokarinsu a wannan fanni.

“Gwamnatin kasar Sin ta kasance kuma ba za ta taba shiga cikin kowane nau’i na taimakon ta’addanci ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

“Zarge-zargen da ke kunshe a cikin rahoton ba su da tushe balle makama, kuma rashin da’a ne, kuma an yi la’akari da manufar rahoton.

“A cikin shekaru da dama da suka gabata, hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen Sin da Nijeriya ya kawo fa’ida ta gaske ga alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kyautata jin dadin jama’ar kasashen biyu.

“Za mu ci gaba da yin aiki tare da gwamnatin Nijeriya don inganta ci gaba da magance matsalolin tsaro, muna maraba da abokan huldar kasa da kasa da su shiga kokarinmu da gaskiya, amma za mu yi watsi da duk wani shiri ko matakin da zai bata mana hadin gwiwa,” in ji ofishin jakadancin a cikin sanarwar.

Rahoton a cikin The Times da aka buga a ranar 15 ga Afrilu, 2023 ya yi ikirarin cewa Beijing na ba da tallafin ta’addanci a kaikaice a Nijeriya don ruguza mafi girman tattalin arziki a Afirka.

A cewar rahoton, shugabannin ma’adinai na kasar Sin suna ba da tallafin kungiyoyin ‘yan ta’addan Nijeriya domin samun damar shiga ma’adinan kasar.

“Kamfanonin China da ke aiki a wasu sassan Nijeriya inda ake yawan kai hare-hare na kulla huldar tsaro da masu tada kayar baya…, in ji wani bangare na rahoton.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.